">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Thursday, October 16, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma Fiye da 30 a Kankara, Jihar Katsina

by Abubakar Ismail kankara
June 23, 2025
in Labarai
0
yan bindiga sun kai hari
Share on FacebookShare on Twitter
">

Yayin da ruwan sama ke sauka a sassan Najeriya, manoma sukan fara shirin noma da farin ciki, amma a Karamar Hukumar Kankara da ke kudancin Jihar Katsina, fargaba da tsoro sun mamaye zukatan al’umma.

‘yan bindiga sun kai hari, inda suka kashe fiye da manoma 30 a ƙauyuka daban-daban da suka haɗa da: Yar Goje, Dan Marke, Burdigau, Gidan Daudu, Gidan Damo, Marmara, Unguwar Tofa, Barebari, Unguwar Gambo, Kwakware, da Santa Dan Geda.

Harin ya auku ne a ranar 16 ga Yuni, 2025. Wasu sun tsira da raunuka sakamakon harbin bindiga, yayin da akayi garkuwa da wasu da dama, kamar yadda wani ganau mai suna Malam Isa (ba sunansa na gaskiya ba) ya shaida wa Jaridar Daily Episode.

A hirarsa da wakilinmu, Malam Isa ya ba da labarin yadda aka harbe abokinsa bayan sun kammala aikin gona.

RelatedPosts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

“Ina zuwa daga nesa don na huta tare da abokina. Cikin sauri na ji harbin bindiga. Na san mun shiga haɗari. Kafin in yi wani yunkuri, tuni suka kewaye Aminu Gurgu. Wasu daga cikinsu suna masa tambayoyi amma daga inda nake a boye, ban iya fahimtar me suke fada masa saboda ina nesa ga kuma fargaba,” in ji Isa.

“Abin bakin ciki, na ga yadda ɗaya daga cikinsu ya harbe Aminu a kai, sannan ya caje aljihunsa, ya sace wayarsa da kuɗinsa, sannan suka nufi kauyen Marmara inda suka kashe wasu ‘yan’uwa guda biyu, Alhaji Isuhu da wani ɗan’uwansa da na manta sunansa ba,” in ji Isa cikin hawaye.

Wani mazaunin kauyen Burdigau, Malam Yakubu Birdigau, ya bayyana wa Daily Episode cewa ‘yan bindigar sun fito ne daga dajin da ke kusa da yankin. Ya ce, “Ko wace shekara ko da zarar ruwan sama ya fara sauka, sai sun kawo hari, su kuma tilasta wasu al’umma su biya haraji kafin su samu damar noma gonakin su.”

Sai dai a wannan karon, lamarin ya fi muni. “Fiye da mutane 30 aka kashe a harin. Hatta gawar mutumin da muka rasa tun farko, sai bayan kwana uku aka samu gawarsa a daji ta kumbura ta fara wari,” in ji Malam Yakubu.

Ya kara da cewa, “Lokacin da aka fara harbin, mun yi zaton jami’an tsaro za su zo ceton mu, amma babu wani ƙoƙari na kawo ɗauki. haka suka gama kashe mutane cikin kwanciyar hankali, babu wanda ya hana ko ya kawo mana agaji.”

“Mun kirga mutane sama da 30 da suka mutu a ƙauyukan Yar Goje, Dan Marke, Burdigau, Gidan Daudu, Gidan Damo, Marmara, Unguwar Tofa, Barebari, Unguwar Gambo, Kwakware da Santa Dan Geda a rana ɗaya. Game da adadin waɗanda aka sace, ba zan iya tabbatar da yawansu ba. Abin takaici ne, gwamnatin ba ta da karfi da zai hana waɗannan hare-hare,” in ji shi.

">

Rundunar ‘yan sandan jihar ba ta fitar da cikakken bayani ba kan harin, duk da alkawarin da kakakin rundunar, DSP Abubakar Sadiq, ya bayar na cewa zai turu mana bayanan bayan da muka tambayeshi.

">

DAILY EPISODE HAUSA

KU BIYO MU A FACEBOOK

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

by Yahuza Bawage
October 6, 2025
0

A wasu yankuna da ke kudancin jihar Kaduna a arewacin Najeriya, mallakar fili, musamman na noma, wani abu ne da...

zaben cike gurbi

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Tun bayan kammala zaben cike gurbi da aka gudanar a fadin kasar nan, rundunar yan sandan jahar ta bayyana irin...

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Duba da yadda rashin magudadan ruwa ke sanadiyar rubtawar kabaruruka musamman a lokutan damina, al’ummar unguwar Dala da kewaye dake...

yunƙurin kashe kansa

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2025
0

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wani mutum mai shekara 50 da aka bayyana sunansa da Modu Isa ya...

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

by Abubakar Ismail kankara
August 16, 2025
0

A dai-dai lokacin da ake fama da yawan yaran da basa zuwa makaranta musamman a fadin arewacin kasar nan, mai...

Tsaro Ya Inganta

Kasa da Awa Ɗaya Bayan Ya Wallafa Cewa Tsaro Ya Inganta, ’Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shi

by Abubakar Ismail kankara
August 15, 2025
0

Rahotan da Daily Episode Hausa ta tattara daka jaridar idon mikiya na nuna da cewa, yan bindiga dake yawan kashe...

Next Post
ƴan sa-kai

Fiye da ƴan Bindiga da ƴan Sa-kai 100 Sun Mutu a Yunkurin Kama Bello Turji a Zamfara

Ganduje

Dalilan Da Suka Tilasta Ganduje Murabus Daga Shugabancin Jam’iyyar APC 

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In