">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Wednesday, October 15, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Yan Uwan Yan Darikar Tijjaniyya 13 da Akayi Garkuwa Dasu a Burkina Faso Sun Roki Shugaba Tinubu da Gwamna Yusuf su Taimaka

by Abubakar Ismail kankara
June 12, 2025
in Labarai
0
Yan Uwan Yan Darikar Tijjaniyya 13 da Akayi Garkuwa Dasu a Burkina Faso Sun Roki Shugaba Tinubu da Gwamna Yusuf su Taimaka
Share on FacebookShare on Twitter
">

Iyalan wasu mabiya darikar Tijjaniyya 13 daga Jihar Kano da aka sace a kasar Burkina Faso kimanin watanni tara da suka gabata sun sake mika kukansu ga Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, da su dauki matakin gaggawa don kubutar da ‘yan uwansu.

Sun kuma bukaci hadin gwiwar Mai baiwa Shugaban kasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu; Sarkin Kano, Alhaji Muhammadu Sanusi II; da kuma shugabannin darikar Tijjaniyya a gida da waje, da su taimaka wajen ganin an sako wadanda aka sace din.

Rahotanni daga PRIME TIME NEWS sun nuna cewa an sace mutanen ne a watan Satumba na shekarar 2024 yayin da suke kan hanyarsu zuwa Kaolak, kasar Senegal, domin halartar babban taron darikar Tijjaniyya.

Wata daga cikin matan da mijinta ke cikin wadanda aka sace, wadda ta bayyana sunanta da Amina, ta bayyana cewa tun bayan bacewar mijinta rayuwa ta gagare ta sosai. A cewarta, tana cikin damuwa da tsananin kunci tun daga lokacin da mijinta ya bace, inda ta ce yanzu tana kokawa da ciyar da ‘ya’yanta uku.

RelatedPosts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

“Duk shekara suna tafiya taron, suna dawowa lafiya. Amma wannan karon ba su dawo ba. Rayuwa ta canza, babu wanda ke kula da mu kamar da. Mutanen da suka fara taimaka mana ma sun fara gajiya,” in ji Amina cikin kunci.

Amina ta roki hukumomi su dauki mataki don ganin an sako mijinta da sauran wadanda aka sace tare da shi.

Shi ma wani dan uwan daya daga cikin mutanen da aka sace, Bashir Tijjani, ya ce tun bayan faruwar lamarin, iyalan mutanen na cikin fargaba da rashin tabbas. Ya ce duk da kokarin da suka yi, ba su samu wata kwakkwarar nasara ko bayanin inda ‘yan uwansu suke ba.

“Sun tashi daga Zawiyyar Sheikh Malam Tijjani ‘Yan Mota a Kano a ranar 7 ga Satumba, sun bi ta Jamhuriyar Nijar zuwa Burkina Faso a hanyarsu ta zuwa Senegal,” in ji Bashir. “Amma a kan iyakar Nijar da Burkina Faso ne wasu ‘yan bindiga suka tare su, suka saki mata uku daga cikin su, suka tafi da maza 13 zuwa daji.”

Ya kara da cewa sun tuntubi shugabannin Tijjaniyya a gida da waje, ciki har da Sarkin Kano, Alhaji Sanusi II, wanda ya tura wakili zuwa Damagaram domin neman bayani daga Sarkin Damagaram. Bayan wannan ganawa, an sanar da ‘yan sanda a Kano, daga bisani kuma an tura batun zuwa Abuja.

Sai dai har zuwa yanzu babu wani sahihin bayani daga bangaren gwamnati ko shugabannin darikar Tijjaniyya kan matakin da aka dauka. Bashir ya yaba da kokarin wasu daidaikun mutane kamar Alhaji Hadi Daura, wanda ya kashe kudinsa wajen kokarin ceto wadanda aka sace.

">

Iyayen wadanda aka sace din suna rokon gwamnati, hukumomin tsaro, da shugabannin addini da su gaggauta daukar mataki don ceto ‘yan uwansu da har yanzu ba a san halin da suke ciki ba.

">

DAILY EPISODE HAUSA

KU BIYO MU A FACEBOOK

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

by Yahuza Bawage
October 6, 2025
0

A wasu yankuna da ke kudancin jihar Kaduna a arewacin Najeriya, mallakar fili, musamman na noma, wani abu ne da...

zaben cike gurbi

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Tun bayan kammala zaben cike gurbi da aka gudanar a fadin kasar nan, rundunar yan sandan jahar ta bayyana irin...

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Duba da yadda rashin magudadan ruwa ke sanadiyar rubtawar kabaruruka musamman a lokutan damina, al’ummar unguwar Dala da kewaye dake...

yunƙurin kashe kansa

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2025
0

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wani mutum mai shekara 50 da aka bayyana sunansa da Modu Isa ya...

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

by Abubakar Ismail kankara
August 16, 2025
0

A dai-dai lokacin da ake fama da yawan yaran da basa zuwa makaranta musamman a fadin arewacin kasar nan, mai...

Tsaro Ya Inganta

Kasa da Awa Ɗaya Bayan Ya Wallafa Cewa Tsaro Ya Inganta, ’Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shi

by Abubakar Ismail kankara
August 15, 2025
0

Rahotan da Daily Episode Hausa ta tattara daka jaridar idon mikiya na nuna da cewa, yan bindiga dake yawan kashe...

Next Post
ƙasurguman ‘yan ta’adda

Sojojin Nijeriya Sun Kashe Auta Da Wasu Manyan ’Yan Ta’adda a Zamfara

Alhazan Nijeriya Sun Yi Zangza-Zanga a Saudiyya

Alhazan Nijeriya Sun Yi Zangza-Zanga a Saudiyya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In