‘Yan bindiga sun yi wa jami’an shige da fice kwanton-bauna, sun kashe mutum 2 a Katsina
Wasu da ake zargin ‘yan fashi ne sun kashe jami’ai biyu na hukumar shige da fice a Katsina yayin wani kwanton bauna da aka yi musu a daren Laraba.
sakamakon binciken ya nuna cewa kwantan baunar ta auku ne a shingen binciken Kadode da ke hanyar Jibia da ke zuwa Jamhuriyar Nijar.
Sunan hafsoshin an bayar da su Umar Bagadaza Kankara da Lauwali Dutse.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar a Katsina, S.I Kasim Iliyasu ya yi alkawarin neman yardar kuma ya dawo.
Amma wani jami’in, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya fadawa majiyar mu cewa “An kai hari kan hukumar kula da bakin haure a shingen binciken kadobe da ke jibia lacal na gwamnatin katsina jami’ai biyu sun rasa rayukansu.”
Jami’in ya ce jami’an sojojin na Najeriya sun taimaka wa jami’an shige da fice wajen dakile harin, wanda ya kai ga mutuwar wasu daga cikin ‘yan fashin.
“Jami’an mu biyu sun mutu yayin da wani soja ya samu rauni.”
Wani dan uwa ga Mista Umar ya fada wa wannan dan jaridar cewa an sanar da dangin rasuwar dan nasu.
“Yayin da nake zantawa da ku, wakilanmu suna kan hanyarsu ta zuwa Katsina don ganawa da jami’an hukumar. An sanar da mu cewa ‘yan bindiga sun kashe shi a daren jiya.”
Duba da wannan dan jaridar ya nuna cewa harin ya faru ne da misalin karfe 12 na safe.