">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Monday, August 18, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Tubabbun Boko Haram sun koma gidan jiya-Zulum

by Abubakar Ismail kankara
March 5, 2021
in Technologies
0
Tubabbun Boko Haram sun koma gidan jiya-Zulum
Share on FacebookShare on Twitter
">

Tubabbun Boko Haram sun koma gidan jiya-Zulum

Gwamnan jihar Borno da ke Najeriya Farfesa Babagana Umara Zulum ya bayyana cewar wasu daga cikin mayakan Boko Haram da suka aje makamansu, aka kuma horar da su wajen sauya tinaninsu  sun koma gidan-jiya, inda suka sake daukar makamai.

Saboda haka Zulum ya bukaci soke shirin da kuma bai wa gwamnatin Najeriya shawarar gurfanar da daukacin wadanda aka kama da zargin shiga ayyukan ta’addanci domin kawo karshen yakin da aka kwashe shekaru 11 ana fafatawa ba tare da kammala shi ba.

Yayin gudanar da taron Kungiyar Gwamnonin da suka fito daga Jihohin Arewa Maso Gabas, Zulum ya bayyana takaicinsa da wannan mataki, inda ya bayyana cewar mayakan Boko Haram na sake dabaru da kuma kai munanan hare-hare.

RelatedPosts

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 6 a Sakkwato

An kama matar da ake zargi da kai wa Bello Turji makamai daji a Zamfara

An Kashe Shahararren Dan Ta’adda Gwaska, Yayin Da Mazauna Yakin Yantumaki Ke Hijira Kan Tarar N30m Da Barazanar Kisa

Shugaba Buhari Ya Bukaci Shugabannin Tsaro Su Kawo Sabbin Dabaru Kan Tsaron Kasar Nan

Gwamnan ya ce tabbas shaidu sun nuna cewar shirin horar da mayakan da suka tuba domin sauya tinaninsu ko kuma ba su damar aje makamai ba ya aiki, ganin yadda a lokaci da dama wadannan mutane da aka horar sun koma sun dauki makamai domin ci gaba da kai hare-hare.

Zulum ya ce horan da tubabbun ke samu na ba su damar fahimtar yadda ake gudanar da harkokin tsaro a yankunan da suke da kuma kai musu hari, yayin da al’ummomi da dama  ba sa bukatar sake karbar irin wadannan mutane saboda fargaba da kuma kallon su a matsayin wadanda suka aikata mummunar laifi a kansu.

Saboda haka Gwamnan ya ce babu dalilin ci gaba da aiwatar da irin wannan shirin kamar yadda ake gudanarwa yanzu, ba tare da sake nazari akan sa ba da kuma nasarar da ake so ya cimma.

">

Zulum ya ce mafita kawai ita ce yi wa irin wadannan mutane shari’a bisa dokar yaki da ta’addanci, yayin da wadanda aka tilastawa shiga kungiyar kawai za a basu damar shiga shirin sake tinaninsu.

">

rfi hausa.

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

hallaka ’yan ta’adda

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 6 a Sakkwato

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Sojojin rundunar Operation Hadarin Daji sun hallaka ’yan ta’adda shida a wani artabu da ya faru a karamar hukumar Gudu,...

An kama matar da ake zargi da kai wa Bello Turji makamai daji a Zamfara

An kama matar da ake zargi da kai wa Bello Turji makamai daji a Zamfara

by Abubakar Ismail kankara
December 30, 2024
0

Bataliyar rundunar sojin Najeriya mai yaƙi da yan fashin daji a arewa maso yammacin Najeriya da ake kira da Operation...

yan bindiga

An Kashe Shahararren Dan Ta’adda Gwaska, Yayin Da Mazauna Yakin Yantumaki Ke Hijira Kan Tarar N30m Da Barazanar Kisa

by Abubakar Ismail kankara
February 11, 2022
0

Sama da mutane dubu daya mazauna kauyen Tashar Biri suka tsere daga kauyen da ke Yatumaki a karamar hukumar Dan...

Buhari Ya Nemi Shugabannin Tsaro Su Kawo Sabbin Dabaru Kan Tsaro

Shugaba Buhari Ya Bukaci Shugabannin Tsaro Su Kawo Sabbin Dabaru Kan Tsaron Kasar Nan

by Maryam Umar Said
September 8, 2021
0

A zaman da ya wakana a jiya Talata a fadar shugaban kasa kan yanayin tsaron kasar nan, shugaba Buhari ya...

Ýan Bindiga Sun Kai Sabon Harin Da Suka Yi Garkuwa Da Mutane 18 A Kaduna

Ýan Bindiga Sun Kai Sabon Harin Da Suka Yi Garkuwa Da Mutane 18 A Kaduna

by Maryam Umar Said
September 7, 2021
0

Ýan bindiga sun kai sabon hari a unguwar Keke da ke Karamar Hukumar Chikun ta Jihar Kaduna. Ýan bindigar sun...

Munyi Rashin Ýan Wasa Amma Hakan Bazai Kawo Mana Naqasu Ba – Ahmad Musa

Munyi Rashin Ýan Wasa Amma Hakan Bazai Kawo Mana Naqasu Ba – Ahmad Musa

by Maryam Umar Said
September 7, 2021
0

Canja shekar da wasu daga cikin ýan wasan kungiyar kwallon kafa ta kasa Super Eagle sukayi bazai kawo naqasu a...

Next Post
Yadda Zaku Nemi daukar Ma’aikatan SUBEB na Jihar Neja 2021

Yadda Zaku Nemi daukar Ma'aikatan SUBEB na Jihar Neja 2021

An Samu Sa Hannun Magu A Badakalar Maina

An Samu Sa Hannun Magu A Badakalar Maina

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In