">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Thursday, October 16, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Sanata Barau ya tura matasa 70 karatu kasar India

by Abubakar Ismail kankara
December 30, 2024
in Sport Stories
0
Sanata Barau ya tura matasa 70 karatu kasar India
Share on FacebookShare on Twitter
">

Sanata Barau Jibrin, mai wakiltar Kano ta Arewa, ya ɗauki nauyin matasa 70 daga jihar Kano don yin karatun digiri na biyu a kasar India.

Wannan shiri na tallafin karatu ya mayar da hankali ne kan bangarorin kimiyya da fasaha, musamman Fasahar zamani (Artificial Intelligence), Kimiyyar Mutumi-mutumi (Robotics), da sauran fannoni na zamani.

Da yake magana a lokacin da yake raka matasan zuwa filin jirgin sama, Sanata Barau ya bayyana cewa manufar wannan shiri shi ne tallafa wa matasa daga gidajen talakawa domin samun ilimin da zai taimakesu da al’ummar baki ɗaya.

“Mun san cewa babban kalubalen Arewa shine rashin ilimi. Yawan matasa albarka ne, amma wannan albarka ba za ta amfani kasa ba sai an basu ilimi mai inganci. Saboda haka, na ɗauki nauyin tura matasa 70 zuwa India domin samun ilimin da zai canza rayuwarsu da ta al’umma gaba ɗaya,” in ji shi.

RelatedPosts

Gobarar Tankar Fetur Ta Yi Ajalin Mutane da Dama a Neja

Iyalan Waɗanda Harin Sojoji ya Shafa a Zamfara Sun Nemi Diyya da Tallafi

Kananan Hukumomi Za Su Fara Karɓar Kuɗaɗensu Kai Tsaye – Fadar Shugaban Ƙasa

Kano Ta Dauki Matakan Gaggawa Kan Rahoton Cutar Murar Tsuntsaye

Sanatan ya kuma bayyana cewa gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu tana ƙoƙarinta wajen tallafa wa yayan talakawa, amma ya ce akwai bukatar masu hannu da shuni su taka rawa wajen inganta harkar ilimi.

“Gwamnati ba za ta iya yin komai ita kaɗai ba. Dole ne masu hali su fito su tallafa. Wannan dalilin ya sa na kafa wannan tsari domin ilimantar da matasanmu,” in ji Sanata Barau.

Sanata Barau ya bayyana cewa ilimi shi ne ginshiƙin ci gaban kowace kasa, inda ya ce: “A duk duniya, babu abinda yake samar da ci gaban tattalin arziki kamar dan Adam mai ilimi da horo. Idan muna da matasa masu ilimi a bangarorin kimiyya da fasaha, to Najeriya za ta amfana matuƙa.”

Sanatan ya kuma ja hankalin matasan da za su amfana da wannan dama cewa su yi kokari wajen kafa nasu masana’antu domin samar da ayyukan yi.

“Muna son ganin matasanmu suna kafa kamfanoni, su zama masu daukar ma’aikata maimakon su jira neman aiki. Za mu tabbatar da cewa bayan sun kammala karatun, za su sami tallafi domin kafa kamfanonin su,” in ji shi.

">

Wannan shiri na tallafin karatu zai zama tsarin shekara-shekara, kuma Sanata Barau ya tabbatar da cewa za a ci gaba da gudanar da shi.

Daya daga cikin wadanda suka amfana da shirin, Salisu Auwal Musa daga karamar hukumar Nasarawa, ya bayyana farin cikinsa da damar da aka bashi.

">

Ya ce:”Ban taɓa fita daga Najeriya ba, amma yanzu ga ni zan je India don yin digiri na biyu a fannin kimiyyar mutumi-mutumi (Robotics Science).

“Wannan dama babbar nasara ce a gare ni da iyalina, kuma na gode wa Sanata Barau bisa wannan taimako.”

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Gobarar Tankar Fetur

Gobarar Tankar Fetur Ta Yi Ajalin Mutane da Dama a Neja

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Mutane da dama, ciki har da wata mai juna biyu, sun rasu yayin da gobara ta tashi lokacin da suke...

harin jiragen Sojin

Iyalan Waɗanda Harin Sojoji ya Shafa a Zamfara Sun Nemi Diyya da Tallafi

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Iyalan waɗanda harin jiragen Sojin saman Najeriya ya rutsa da su a Zamfara sun nemi gwamnati ta biya su diyya...

Asusun Bai Ɗaya

Kananan Hukumomi Za Su Fara Karɓar Kuɗaɗensu Kai Tsaye – Fadar Shugaban Ƙasa

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Fadar shugaban ƙasa ta sanar da cewa, daga ƙarshen watan Janairu, dukkan kananan hukumomi a Najeriya za su fara karɓar...

Murar Tsuntsaye

Kano Ta Dauki Matakan Gaggawa Kan Rahoton Cutar Murar Tsuntsaye

by Abubakar Ismail kankara
January 17, 2025
0

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta yi kira ga al’umma da su kwantar da hankali tare da kai rahoton duk...

Biden da Netanyahu sun tattauna kan tsagaita wuta a Gaza

Biden da Netanyahu sun tattauna kan tsagaita wuta a Gaza

by Abubakar Ismail kankara
January 13, 2025
0

Shugaban Amurka, Joe Biden da Firaiministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu sun tattauna ta waya a daidai lokacin da ake ci gaba...

rikicin masarautar Kano

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Umarci Sake Sauraron Shari’ar Rikicin Masarautar Kano

by Abubakar Ismail kankara
January 10, 2025
0

Kotun ɗaukaka ƙara da ke Abuja ta bayar da umarnin sake sauraron shari’ar rikicin masarautar Kano da ya haɗa da...

Next Post
Hukumar Hisbah Ta Fara Kauda Yara Masu Gara-Ranba Daga Titunan Kano

Hukumar Hisbah Ta Fara Kauda Yara Masu Gara-Ranba Daga Titunan Kano

Da dumi’dumi: Gwamna Sule ya kori dukkan kwamishinonin sa tare da Sakataren Gwamnatin Jihar.

Da dumi'dumi: Gwamna Sule ya kori dukkan kwamishinonin sa tare da Sakataren Gwamnatin Jihar.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In