">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Thursday, October 16, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Kungiyar CAN Ta Yi Kiran A Kama Sheikh Gumi

by Abubakar Ismail kankara
March 4, 2021
in Sport Stories
0
Share on FacebookShare on Twitter
">

RelatedPosts

Gobarar Tankar Fetur Ta Yi Ajalin Mutane da Dama a Neja

Iyalan Waɗanda Harin Sojoji ya Shafa a Zamfara Sun Nemi Diyya da Tallafi

Kananan Hukumomi Za Su Fara Karɓar Kuɗaɗensu Kai Tsaye – Fadar Shugaban Ƙasa

Kano Ta Dauki Matakan Gaggawa Kan Rahoton Cutar Murar Tsuntsaye

">
">

Kungiyar Kiristocin Najeriya ta Ƙasa CAN tayi kira da babbar murya da cewar cikin gaggawa ba tare da ɓata lokaci ba Gwamnati ta yi gaggawar kama Malamin Addinin Musulunci Dr. Ahmad Abubakar Mahmoud Gumi, saboda kalaman shi da yake furtawa masu alaka da sha’anin tsaro na ƙasa.

CAN ta nuna damuwarta cewa shirun da Shugaba Muhammadu Buhari ya yi na tsawon lokaci game da wasu maganganun kwanan nan da shahararren malamin addinin Islama, Sheikh Ahmad Gumi ya yi, yana nufin amincewa da ikirarin nasa.

Daya daga cikin irin wadannan ikirarin na Gumi shi ne cewa sojoji kirista su ne ke kashe ‘yan Bindiga da sauran masu tayar da kayar baya a kasar nan.

Ƙungiyar kiristocin ta yi kira ga Gumi da ya janye “kalaman rashin kishin kasa da rarrabuwa” da aka alakanta da shi domin neman zaman lafiya da hadin kan kasar. Idan da Sheikh Gumi Kirista ne, da gwamnatin Buhari ta yi Allah wadai da kalamansa, sannan ta kame shi.

Sanarwar wacce babban sakataren Kungiyar CAN din, Joseph Daramola, ya sanya wa hannu ya ce, “Idan wani ya ce sojojin Kirista ne ke kai hari ga ‘yan bindiga, wannan mutumin ba ya fatan kasar nan da alheri kuma ba ya son yaki da ta’addanci da’ yan ta’adda ya ƙare cikin nasara.

“Ba za a iya ɗaukar hujjar murya ta Gumi da muhimmanci ba saboda ana iya shirya shaidar sautin murya da gangan don kafa hujja. Abu na biyu, ta yaya za mu iya tabbatar da amincin mutumin da ke zargin cewa sojojin Kirista ne ke kai hari ga garuruwa da ‘yan Bindiga?

“Wannan ikirarin da bai dace ba, baya ga bacin rai da raba kan rundunar sojin Najeriya da zai yi gida biyu ta ɓangaren addini, zai kuma bata martabar sojojin da ba kirista ba a matsayin wadanda basu jajirce wajen yaki da ta’addanci ba.

“Shirun da Shugaba Muhammadu Buhari ya yi na tsawon lokaci daidai yake da amincewa da furucin Gumi mai hadari. Idan da za a danganta abin da Gumi ya fada ga shugaban kirista, da jami’an tsaro sun gayyace shi ko kuma su bayyana shi a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo, kuma da Fadar Shugaban kasa ta yi Allah wadai da wannan shugaban na Kirista.

“Mun tuna yadda jami’an tsaro suka yi da kalaman Dr Obadiah Mailafia, Prophet Isa El-Buba da kuma na baya-bayan nan, Shugaban Katolika Dr Matthew Hassan Kukah sannan gwamnati ma ta yi martani. Shin da gaske muna da tsarkakkun da ba a tabawa a kasar yanzu?”

A gefe guda, Kungiyar matasan Ibo ta ‘The Ohanaeze Ndigbo Youth Council, OYC,’ ta bukaci a kama malamin addinin musulunci da ke kokarin yin sulhu da yan bindiga a arewacin Najeriya, Sheikh Ahmad Gumi nan take ba tare da ɓata lokaci ba.

Gumi ya fusata kungiyar ta Igbo ne sakamakon kwatanta shugaban Ibo, marigayi Dim Chukwuemeka Odumegwu Ojukwu da ‘yan bindiga a hirar da aka yi da shi a BBC Pidgin.

Ojukwu ne ya jagorancin kabilar Ibo yayin yakin basasar Nijeriya da aka shafe shekaru uku ana gwabzawa wadda ta yi sanadin salwantar miliyoyin rayuka da tarin dukiya mara adadi.kuma na ganin laifin da Ojukwu ya yi ta yi kama da na yan bindiga.

DAILY EPISODE HAUSA

KU BIYO MU A FACEBOOK DA TWITTER

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Gobarar Tankar Fetur

Gobarar Tankar Fetur Ta Yi Ajalin Mutane da Dama a Neja

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Mutane da dama, ciki har da wata mai juna biyu, sun rasu yayin da gobara ta tashi lokacin da suke...

harin jiragen Sojin

Iyalan Waɗanda Harin Sojoji ya Shafa a Zamfara Sun Nemi Diyya da Tallafi

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Iyalan waɗanda harin jiragen Sojin saman Najeriya ya rutsa da su a Zamfara sun nemi gwamnati ta biya su diyya...

Asusun Bai Ɗaya

Kananan Hukumomi Za Su Fara Karɓar Kuɗaɗensu Kai Tsaye – Fadar Shugaban Ƙasa

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Fadar shugaban ƙasa ta sanar da cewa, daga ƙarshen watan Janairu, dukkan kananan hukumomi a Najeriya za su fara karɓar...

Murar Tsuntsaye

Kano Ta Dauki Matakan Gaggawa Kan Rahoton Cutar Murar Tsuntsaye

by Abubakar Ismail kankara
January 17, 2025
0

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta yi kira ga al’umma da su kwantar da hankali tare da kai rahoton duk...

Biden da Netanyahu sun tattauna kan tsagaita wuta a Gaza

Biden da Netanyahu sun tattauna kan tsagaita wuta a Gaza

by Abubakar Ismail kankara
January 13, 2025
0

Shugaban Amurka, Joe Biden da Firaiministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu sun tattauna ta waya a daidai lokacin da ake ci gaba...

rikicin masarautar Kano

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Umarci Sake Sauraron Shari’ar Rikicin Masarautar Kano

by Abubakar Ismail kankara
January 10, 2025
0

Kotun ɗaukaka ƙara da ke Abuja ta bayar da umarnin sake sauraron shari’ar rikicin masarautar Kano da ya haɗa da...

Next Post
Zan Kunyata Malaman Kano Ranar Muƙabala – AbdulJabbar Kabara

Jama’atu Nasril Islam Ba Zata Halarci Mukabala Da Abdul-Jabbar Ba

‘Yan bindiga sun sace mutum 60 sun kona garin Ruwan Tofa a Zamfara

‘Yan bindiga sun sace mutum 60 sun kona garin Ruwan Tofa a Zamfara

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In