">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Sunday, October 12, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Jama’atu Nasril Islam Ba Zata Halarci Mukabala Da Abdul-Jabbar Ba

by Abubakar Ismail kankara
March 4, 2021
in Uncategorized
0
Zan Kunyata Malaman Kano Ranar Muƙabala – AbdulJabbar Kabara
Share on FacebookShare on Twitter
">

Kungiyar Jama’atu Nasril Islam ta ƙasa ƙarƙashin jagorancin Shugabanta mai alfarma Sarkin Musulmi Dr Sa’adu Abubakar, ta bayyana cewar ba zata samu damar halartar mukabala da gwamnatin Kano ta shirya gudanarwa tsakanin Abdul-Jabbar da Malaman Kano ba.

Kungiyar ta bayyana hakan ne a cikin wata takardar sanarwa da ta samu sanya hannun babban Sakataren Ƙungiyar Dr Khalid Abubakar Aliyu, kuma aka rarraba ta ga manema labarai a Kaduna.

Kungiyar ta Jama’atu ta bayyana kalaman da Abdul-Jabbar ke amfani da su a janibin Manzon Allah SAW da Sahabbai, a matsayin cin mutuncin da taɓa darajar Annabi SAW, bisa ga haka hatsari ne babba a gudanar da zama da mutumin da ke irin wadannan miyagun maganganu.

“Babu mai shakkar katoɓarar da Abdul-Jabbar ke yi ga janibin Manzon Allah, gudanar da zama da shi akan hakan kamar taimaka mishi ne wajen yaɗa kalamanshi munana akan Manzon Allah, bisa ga haka Jama’atu ba zata halarci zaman ba, hakazalika dukkanin rassan Ƙungiyar dake Jihohi”

RelatedPosts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

“Kungiyar ta Jama’atu tun da fari ta yaba matakin da gwamnatin Kano ta ɗauka na daƙile dukkanin wata fitina da ka iya tasowa ta dalilin kalaman AbdulJabbar, amma duk da haka ya kamata gwamnatin ta sake faɗaɗa tunaninta akai, domin kuwa wannan al’amari ne babba ba jihar Kano ko Najeriya kadai ya shafa ba, babban al’amari ne da ya shafi duniya gaba daya ya dace a kiyaye”.

Kungiyar ta Jama’atu ta kuma yi fatan alkhairi ga malaman da zasu halarci zaman muƙabalar da yi musu kyakkyawar fata, amma duk da haka tana ƙara kira ga Gwamnatin jihar Kano da sake nazari da yin duba akan matsayin da ta ɗauka.

">

Abdul-Jabbar Nasiru Kabara dai na fuskantar suka daga ɓangarorin Malamai a jihar Kano bisa ga yadda yake gudanar da karatuttukan shi, lamarin da Malaman ke gani ya yi hannun riga da yadda tsarin karantarwar take tun asali.

Daga bisani ne Gwamnatin Jihar Kano ta shigo cikin lamarin har ta kai ga kulle Masallachin da Abdul-Jabbar ke gudanar da karatu tare da shirya gudanar da mukabala tsakanin shi da sauran malamai, wanda aka tsara yi a ranar Lahadi mai zuwa 07 ga wannan wata na Maris da muke ciki a birnin Kano.

 

DAILY EPISODE HAUSA

KU BIYO MU A FACEBOOK DA TWITTER

">
Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

by Yahuza Bawage
October 6, 2025
0

A wasu yankuna da ke kudancin jihar Kaduna a arewacin Najeriya, mallakar fili, musamman na noma, wani abu ne da...

zaben cike gurbi

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Tun bayan kammala zaben cike gurbi da aka gudanar a fadin kasar nan, rundunar yan sandan jahar ta bayyana irin...

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Duba da yadda rashin magudadan ruwa ke sanadiyar rubtawar kabaruruka musamman a lokutan damina, al’ummar unguwar Dala da kewaye dake...

yunƙurin kashe kansa

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2025
0

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wani mutum mai shekara 50 da aka bayyana sunansa da Modu Isa ya...

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

by Abubakar Ismail kankara
August 16, 2025
0

A dai-dai lokacin da ake fama da yawan yaran da basa zuwa makaranta musamman a fadin arewacin kasar nan, mai...

Tsaro Ya Inganta

Kasa da Awa Ɗaya Bayan Ya Wallafa Cewa Tsaro Ya Inganta, ’Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shi

by Abubakar Ismail kankara
August 15, 2025
0

Rahotan da Daily Episode Hausa ta tattara daka jaridar idon mikiya na nuna da cewa, yan bindiga dake yawan kashe...

Next Post
‘Yan bindiga sun sace mutum 60 sun kona garin Ruwan Tofa a Zamfara

‘Yan bindiga sun sace mutum 60 sun kona garin Ruwan Tofa a Zamfara

Tubabbun Boko Haram sun koma gidan jiya-Zulum

Tubabbun Boko Haram sun koma gidan jiya-Zulum

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In