">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Saturday, October 11, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Haryanzu Ba’a Ga Mutane Sama da 700 Ba Tun Bayan  Ambaliya a Mokwa – Gwamnatin Neja 

by Abubakar Ismail kankara
June 18, 2025
in Labarai
0
mummunar ambaliya
Share on FacebookShare on Twitter
">

Gwamnatin Jihar Neja ta bayyana cewa fiye da mutane 700 har yanzu ba a gansu ba bayan mummunar ambaliya da ta afku a karamar hukumar Mokwa na jihar.

Gwamna Umaru Bago ne ya bayyana haka a lokacin da ya karɓi bakuncin Manjo Hamza Al-Mustapha, tsohon jami’in tsaron marigayi Janar Sani Abacha, da wasu abokansa da suka kai ziyarar jaje bisa ibtila’in ambaliyar da ta auku a Minna a ranar Talata.

Gwamnan wanda mataimakinsa, Yakubu Garba ya wakilta, ya ce mutane 207 sun mutu, kana gidaje fiye da 3,000 sun lalace sakamakon iftila’in.

“Fiye da mutane 700 sun bace kuma har yanzu ba mu san inda suke ba. Ambaliyar ta haifar da barna mai yawa,” in ji Gwamna Bago.

Ya ƙara da cewa, gidaje 400 sun samu lahani, inda 283 daga ciki suka rushe gaba ɗaya, har da shaguna 50 da aka lalata.

RelatedPosts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

Gwamnan ya gode wa mutane da hukumomi da suka kawo gudunmawa da agaji, yana mai cewa wannan bala’i ya shafi kasa baki ɗaya, ba jihar Neja kawai ba.

Ya ce gwamnati na aiki da masana don gano musabbabin ambaliyar, kuma ana jiran sakamakon binciken.

A nasa jawabin, Hamza Al-Mustapha ya ce sun zo ne domin yi wa gwamnatin Neja da mutanen Mokwa ta’aziyya bisa iftila’in da ya faru.

“Mun zo ne don nuna alhini bisa asarar rayuka da dukiyoyi. Muna fatan hakan ba zai kara faruwa ba,” in ji shi.

Ya ce tawagar ta kunshi manyan mutane daga sassa daban-daban na kasar, kuma sun zo ne da niyyar ba da tallafi da shawarwari ga gwamnati da al’umma.

Ya bayyana cewa za su gana da majalisar gargajiya ta Mokwa, don tattaunawa kan hanyoyin da za a magance irin wannan iftila’i a nan gaba tare da inganta tsare-tsaren birane da yanayin zama.

Bayan haka, Al-Mustapha da tawagarsa sun kai ziyara ta girmamawa ga tsohon shugaban mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (rtd.).

">

DAILY EPISODE HAUSA

">

KU BIYO MU A FACEBOOK

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

by Yahuza Bawage
October 6, 2025
0

A wasu yankuna da ke kudancin jihar Kaduna a arewacin Najeriya, mallakar fili, musamman na noma, wani abu ne da...

zaben cike gurbi

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Tun bayan kammala zaben cike gurbi da aka gudanar a fadin kasar nan, rundunar yan sandan jahar ta bayyana irin...

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Duba da yadda rashin magudadan ruwa ke sanadiyar rubtawar kabaruruka musamman a lokutan damina, al’ummar unguwar Dala da kewaye dake...

yunƙurin kashe kansa

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2025
0

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wani mutum mai shekara 50 da aka bayyana sunansa da Modu Isa ya...

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

by Abubakar Ismail kankara
August 16, 2025
0

A dai-dai lokacin da ake fama da yawan yaran da basa zuwa makaranta musamman a fadin arewacin kasar nan, mai...

Tsaro Ya Inganta

Kasa da Awa Ɗaya Bayan Ya Wallafa Cewa Tsaro Ya Inganta, ’Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shi

by Abubakar Ismail kankara
August 15, 2025
0

Rahotan da Daily Episode Hausa ta tattara daka jaridar idon mikiya na nuna da cewa, yan bindiga dake yawan kashe...

Next Post
MAGANIN BARAYIN WAYA

MAGANIN BARAYIN WAYA

Rokon Ruwan Sama

An Gudanar da Sallar Rokon Ruwan Sama a Kaura Namoda - Jihar Zamafara

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In