">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Wednesday, October 15, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Gwamnati Ta Kaddamar da Shirin TVET Don Horas da Matasa Kyauta, Tare da Biyan Naira 22,500 Kowane Wata

by Abubakar Ismail kankara
June 18, 2025
in Labarai
0
TVET
Share on FacebookShare on Twitter
">

Bayan kafa tsarin bashi ga ɗaliban Najeriya, wanda nufinsa shi ne bai wa matasa damar samun ilimi cikin sauƙi da kuma hana barin makaranta, gwamnatin tarayya ta ƙara ɗaukar mataki ta hanyar ƙaddamar da sabon shirin TVET domin koyar da matasa da ɗalibai dabarun sana’a da basira don su sami nasara a rayuwa.

A wajen wani taron wayar da kan al’umma da aka gudanar a Kaduna, wanda kamfanin G-Adams Integrated Service Limited ya shirya ƙarƙashin taken: “Matasa ta Hanyar Kwarewa: Sabuwar Fuskar TVET a Najeriya”, Daraktan Ayyuka na Shirin, Mustafa Iyal, ya bayyana yadda shirin ke da burin magance matsalar rashin aikin yi a ƙasar.

A cewarsa: “A Najeriya, mun saba da shirye-shiryen kasuwanci da koyon sana’a, amma idan aka duba tsarin da dabarun da aka gina wannan shiri da su, zan iya tabbatar muku cewa wannan na daga cikin mafi inganci da ƙasar nan ta taɓa samu, duba da irin tasirin da zai haifar a cikin ƴan shekaru masu zuwa.”

“TVET yana da rassa guda uku: Na farko, akwai ‘master twelve’ wanda yana ɗaukar shekara guda inda kowane mai nema zai sami horo na cikakken shekara. Sai kuma ‘master six’ wanda zai ɗauki tsawon shekaru shida. A ƙarshe kuma, akwai shirin federal technical colleges tracking, wanda manufarsa ita ce taimaka wa makarantun fasaha da ɗalibansu don ƙara inganci da samar da ayyukan yi,” in ji Iyal.

RelatedPosts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

Ya ƙara da cewa horon kyauta ne gaba ɗaya, kuma an haɗa ƙwararrun ƙungiyoyi da dama a cikin shirin, yana kuma roƙon jama’a su amfana da wannan dama.

“An tanadar da horo kyauta gaba ɗaya. Gwamnati za ta biya kuɗin horon, sannan kuma za ta rika biyan kowane mahalarta ₦20,000 a kowane wata a matsayin alawus. Bayan kammala horon, za a ba su kayan aiki da na’ura a matsayin jari don fara sana’arsu,” in ji shi.

“Wannan dama ce ga kowane ɗan Najeriya, ko daga Arewa ko Kudu, matuƙar kana da ƙasar nan, kana da damar neman shiga shirin TVET.”

Ya ƙara da cewa abubuwan da ake buƙata domin shiga shirin ba su da yawa. “Kawai katin shaida na ƙasa (NIMC), lambar waya, da kuma BVN kawai ake buƙata,” in ji shi.

A ƙarshe, Mr. Iyal ya yi kira ga ƴan Najeriya da su rungumi shirin TVET domin ci gaban ƙasa.

">
">

DAILY EPISODE HAUSA

KU BIYO MU A FACEBOOK

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

by Yahuza Bawage
October 6, 2025
0

A wasu yankuna da ke kudancin jihar Kaduna a arewacin Najeriya, mallakar fili, musamman na noma, wani abu ne da...

zaben cike gurbi

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Tun bayan kammala zaben cike gurbi da aka gudanar a fadin kasar nan, rundunar yan sandan jahar ta bayyana irin...

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Duba da yadda rashin magudadan ruwa ke sanadiyar rubtawar kabaruruka musamman a lokutan damina, al’ummar unguwar Dala da kewaye dake...

yunƙurin kashe kansa

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2025
0

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wani mutum mai shekara 50 da aka bayyana sunansa da Modu Isa ya...

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

by Abubakar Ismail kankara
August 16, 2025
0

A dai-dai lokacin da ake fama da yawan yaran da basa zuwa makaranta musamman a fadin arewacin kasar nan, mai...

Tsaro Ya Inganta

Kasa da Awa Ɗaya Bayan Ya Wallafa Cewa Tsaro Ya Inganta, ’Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shi

by Abubakar Ismail kankara
August 15, 2025
0

Rahotan da Daily Episode Hausa ta tattara daka jaridar idon mikiya na nuna da cewa, yan bindiga dake yawan kashe...

Next Post
yan sandan Jihar Neja

'Yan Sanda Sun Kama Wasu Yan Bindiga Biyu Dake Yunkurin Sace Wani Mutum a Tafa, Jihar Neja

mummunar ambaliya

Haryanzu Ba'a Ga Mutane Sama da 700 Ba Tun Bayan  Ambaliya a Mokwa - Gwamnatin Neja 

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In