">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Thursday, October 16, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Fiye da ƴan Bindiga da ƴan Sa-kai 100 Sun Mutu a Yunkurin Kama Bello Turji a Zamfara

by Abubakar Ismail kankara
June 25, 2025
in Labarai
0
ƴan sa-kai
Share on FacebookShare on Twitter
">

SHINKAFI, JIHAR ZAMFARA — Rikici mai tsanani da ya ɓarke tsakanin ɗan bindiga da aka fi sani da Bello Turji da kuma jami’an tsaro na sa-kai a Zamfara Civilian Protection Guard (CPG) ya yi sanadiyyar mutuwar fiye da mutane 100 a kusa da kauyen Cida da ke ƙaramar hukumar Shinkafi.

Wani mazaunin yankin, Sa’idu Garba, ya shaida wa Jaridar Punch cewa ƴan sa-kai daga Zamfara da taimakon ƴan sa-kai na mai duguri wato (CJTF), sun ƙaddamar da wani hari a sansanin Turji ba tare da sahalewar hukumomin tsaro ba, da nufin kama shi kai tsaye—rai ko a mace.

An bayyana cewa wani tsohon ɗan bindiga da ya tuba, Bashari Meniyo, ne ya jagoranci harin.

“Sun tara kansu bisa jagorancin Bashari Meniyo, suka nufi sansanin Turji kai tsaye ba tare da sanar da jami’an tsaro ba,” in ji Garba. “Turji ya samu labari kafin su iso, sai ya tara fiye da mayaka dubun guda don kare kansa.”

RelatedPosts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

Lamarin ya rikide zuwa faɗa mai zafi da aka shafe sa’o’i ana musayar wuta, inda aka kashe mutane da dama, ciki har da Bashari Meniyo da wasu daga cikin tawagarsa.

Wani mazaunin garin, Mohammed Sani, ya ce an ji karar bindigada da harbe-harbe da dama a ranar Litinin, kuma lamarin ya tayar da hankalin mazauna yankin.

“Mutane sun farka da karar bindiga, kowanne na neman mafaka, suna tserewa cikin daji domin tsira da rayuwarsu,” in ji shi. “Faɗar ta daɗe sosai ba tare da jami’an tsaro sun shigo sun kaw agaji ga yan sakai din ba.”

Garba ya bayyana takaicinsa kan rashin saurin daukar matakin hukumomin tsaro. “Da an zo cikin lokaci, da Bello Turji ya shiga hannun,” in ji shi.

Kokarin jin ta bakin jami’an tsaro ya ci tura, domin Lt. Col. Suleiman Omale, mai magana da yawun rundunar soji a jihar, bai amsa kiran waya ko saƙonnin da aka tura masa ba.

">

Sai dai mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Mustafa Kaura, ya tabbatar da afkuwar lamarin, sai dai ya ce bai da tabbacin adadin mutanen da suka mutu ba.

“Ina da tabbacin cewa lamarin ya faru, amma har yanzu ba ni da cikakken bayani kan yawan waɗanda suka rasa rayukansu. Ana gudanar da bincike,” in ji Kaura.

Rikicin dai ya ƙara jefa yankin cikin fargaba, inda al’umma ke ƙara rasa kwanciyar hankali sakamakon yawaitar hare-haren da ‘yan bindiga ke kai wa a sassan jihar.

">

DAILY EPISODE HAUSA

KU BIYO MU A FACEBOOK

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

by Yahuza Bawage
October 6, 2025
0

A wasu yankuna da ke kudancin jihar Kaduna a arewacin Najeriya, mallakar fili, musamman na noma, wani abu ne da...

zaben cike gurbi

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Tun bayan kammala zaben cike gurbi da aka gudanar a fadin kasar nan, rundunar yan sandan jahar ta bayyana irin...

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Duba da yadda rashin magudadan ruwa ke sanadiyar rubtawar kabaruruka musamman a lokutan damina, al’ummar unguwar Dala da kewaye dake...

yunƙurin kashe kansa

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2025
0

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wani mutum mai shekara 50 da aka bayyana sunansa da Modu Isa ya...

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

by Abubakar Ismail kankara
August 16, 2025
0

A dai-dai lokacin da ake fama da yawan yaran da basa zuwa makaranta musamman a fadin arewacin kasar nan, mai...

Tsaro Ya Inganta

Kasa da Awa Ɗaya Bayan Ya Wallafa Cewa Tsaro Ya Inganta, ’Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shi

by Abubakar Ismail kankara
August 15, 2025
0

Rahotan da Daily Episode Hausa ta tattara daka jaridar idon mikiya na nuna da cewa, yan bindiga dake yawan kashe...

Next Post
Ganduje

Dalilan Da Suka Tilasta Ganduje Murabus Daga Shugabancin Jam’iyyar APC 

Marigayi Alhaji Aminu Dantata

Gwamnatin Saudiyya Ta Amince a  Binne Marigayi Alhaji Aminu Dantata a Madina

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In