">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Tuesday, October 14, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

by Yahuza Bawage
October 6, 2025
in Aiki/Sana'a, Labarai
0
Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’
Share on FacebookShare on Twitter
">

A wasu yankuna da ke kudancin jihar Kaduna a arewacin Najeriya, mallakar fili, musamman na noma, wani abu ne da mata ba su fiya samu ba. Hakan kuma, na da alaƙa da al’adun yankin, kamar na ƙabilar Bajju, inda maza ne kaɗai ke da haƙƙin mallakar fili ta hanyar gado.

Martha Saleh, ɗaya ce daga cikin matan da suka fuskanci irin wannan ƙalubale har na tsawon shekaru. 

Ta ce wasu lokutan takan tuna yadda ita da sauran matan da ke zaune a Anguwan Mission a ƙaramar hukumar Zongon-Kataf suke tafiya ƙauyen One Man Village mai nisan awa ɗaya don neman kwangilar aikatau a gonakin da ba nasu ba. 

“A lokacin ladan aikinmu na kamawa daga ₦2,000 zuwa ₦10,000 a kowace rana,” a cewar Martha.

RelatedPosts

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Abin da suke samu a lokacin bai wuce na ciyar da iyalansu ba, balle har ya isa su iya gina wani abu na kansu.

A wata safiya a shekarar 2015, Martha ta tara wasu mata 19 a ƙarƙashin wata bishiyar mangwaro a Anguwan Mission ta faɗa musu cewa lokaci ya yi da za su fita daga wannan ƙangi na wahala.

A ranar suka cimma yarjejiniyar kafa ƙungiyar da suka sa wa suna “Ci Gaban Taimakon Mata”.

Sun kuma yarda cewa duk kuɗin da suka samu daga yin aikatau a gonaki, za su adana shi cikin asusun ajiyar kuɗi na haɗin gwiwa. 

Sa’annan, a ƙarshen kowane wata, za a raba kuɗin daidai wa daida.

Cikin shekaru biyu, hoɓɓasarsu ta kai ga tara kuɗade masu yawa, wanda a ciki ne kuma kowace mamba ta ƙungiyar ta samu damar sayan filin noma. Hakan ya samu ne da haɗin kan dagatai daga yankin.

“Kimanin ₦80,000 na sayi nawa filin. Yanzu filin da ke da girman nawa zai kai ₦500,000,” in ji Martha.

Agnes Stephen, wata mamba a ƙungiyar, ta ce ita ta sayi nata kan ₦70,000.

Mallakar filin noma da Martha da sauran matan suka yi, nasara ce da ake ganin ta zama abin koyi a ƙasar da mata ke yin sama da kashi 70 na aikin gona amma ke mallakar ƙalilan na filayen noma, kamar yadda Shirin Ƙarfafa Tattalin Arzikin Matan Najeriya na 2023 (WEE Policy) ya nuna.

Har ila yau, nasarar ba ta gama kai wa ga kowa ba. Hannatu, wata mata daga Kachia, a jihar Kaduna, ta rasa gonar mijinta bayan rasuwarsa a shekarar 2022, inda ƴan uwan mijin nata suka ƙwace filin saboda a al’adarsu su ke da haƙƙin gadon filin. 

Yanzu dai an bar Hannatu da neman aikin aikatau a gonakin mutane domin ta samu ta ciyar da ƴaƴanta.

Maryam Musa Gusau, wata lauya a Kaduna, ta ce babu wani sashe a Dokar Amfani da Fili (Land Use Act) ta 1978 da ya hana mace mallakar fili. “Dokar ta ce kowanne mutum zai iya mallakar fili, walau mace ko namiji,” in ji ta.

">

“Duk wata al’ada da ta saɓa wa kundin tsarin mulki ba ta da tushe,” in ji lauya Maryam.

Ta ƙara da cewa a duk inda aka tauye wa mata haƙƙinsu na mallakar filayen noma, suna iya shigar da ƙara a kotu don samun adalci.

Sai dai, a cewar Martha, mata da yawa ba sa zuwa kotu saboda tsoron samun rashin jituwa tsakanin matan da ƴan uwansu da kuma rashin kuɗi.

A ƙoƙarinta na shawo kan matsalolin da mata ke fuskanta, gwamnatin jihar Kaduna ta ƙaddamar da Shirin Ƙarfafa Tattalin Arzikin Mata (WEE Policy) a watan Nuwamba shekarar 2024. Kuma ta yi alƙawarin taimaka wa mata 15,000 ta hanyar ƙungiyoyi 750 da kuɗin tallafi da ya kai naira biliyan biyar. 

Martha da mambobin ƙungiyarta sun halarci taron horo da gwamnatin jihar ta jagoranta inda aka gaya musu su yi rijistar ƙungiyarsu don samun wannan tallafi. 

“Mun cika takardu kamar yadda suka ce. Yanzu muna jira,” in ji Shattu Ɗanladi, mai muƙamin ma’aji a ƙungiyar.

Sai dai duk da wannan ci gaba, waɗannan mata har yanzu suna fuskantar ƙalubale, inda aikace-aikacen gida ke daƙile ƙoƙarinsu na faɗaɗa gonakinsu wajen noma da girban amfani mai yawa.

A wani ɓangaren, rashin wadataccen takin zamani ma wani abu ne da ke ci musu tuwo a ƙwarya.

Hakan na da nasaba da tashin gwauron zabo da taki ya yi a wannan shekarar, inda kuɗin buhun urea kilo 50 ya tashi daga ₦37,000 a bara zuwa ₦50,000 yanzu.

A cewar manoma, nau’in NPK 20:10:10 yana kai wa ₦10,000 zuwa ₦30,000.

Gwamnatin jihar Kaduna dai a watan Agusta ta raba takin zamani kyauta ga manoma 100,000 a fadin jihar. Amma mata da ke ƙungiyar su Martha ba su samu ba.

“Sun ce sun raba, amma mu dai bai iso gare mu ba,” in ji Shattu.

">

Bugu da ƙari, ta ce idan za ta sayi taki da zai ishi gonakinta guda biyu, sai ta kashe kusan duk kuɗin da ta samu a kakar noma da ya wuce.

Yanzu dai matan na amfani da kashin shanu a matsayin taki.

Da wannan ne Martha ke girbe buhu 50 na masara a kowace kaka. Ta ce idan ta sayar da amfanin da ta girbe, tana amfani da kuɗin wajen biyan kuɗin makarantar ƴaƴanta.

“Bayan girbi, muna ware kaso daga abin da aka girbe don taimaka wa iyalai da ba su da abinci,” in ji Shattu. “Kuma muna tallafa wa ɗalibai marasa galihu da littatafan rubutu na makaranta.”

Agnes ma ta ce bara ta sayar da gyaɗar da ta girbe ta biya kuɗin jinyar yaronta da ba shi da lafiya ba tare da ta ranci kuɗi ba.

“Ina jin farin ciki duk lokacin da na tuna cewa ina da gona ta kai na,” in ji Agnes.

An shirya wannan rahoto ne da tallafin ƙungiyar Solutions Journalism Network da kuma Gidauniyar Hewlett, a ƙarƙashin Shirin Tattara Labarai Kan Daidaito Tsakanin Maza da Mata wanda Gidauniyar Watsa Labarai da Ci Gaba ta Social Voices ta samar.

DAILY EPISODE HAUSA

KU BIYO MU A FACEBOOK 

Yahuza Bawage

Yahuza Bawage

Related Posts

zaben cike gurbi

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Tun bayan kammala zaben cike gurbi da aka gudanar a fadin kasar nan, rundunar yan sandan jahar ta bayyana irin...

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Duba da yadda rashin magudadan ruwa ke sanadiyar rubtawar kabaruruka musamman a lokutan damina, al’ummar unguwar Dala da kewaye dake...

yunƙurin kashe kansa

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2025
0

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wani mutum mai shekara 50 da aka bayyana sunansa da Modu Isa ya...

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

by Abubakar Ismail kankara
August 16, 2025
0

A dai-dai lokacin da ake fama da yawan yaran da basa zuwa makaranta musamman a fadin arewacin kasar nan, mai...

Tsaro Ya Inganta

Kasa da Awa Ɗaya Bayan Ya Wallafa Cewa Tsaro Ya Inganta, ’Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shi

by Abubakar Ismail kankara
August 15, 2025
0

Rahotan da Daily Episode Hausa ta tattara daka jaridar idon mikiya na nuna da cewa, yan bindiga dake yawan kashe...

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wadanda Suka Kashe Tsohon Kwamishina a Katsina

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wadanda Suka Kashe Tsohon Kwamishina a Katsina

by Humaira Muhammad
July 30, 2025
0

Babbar Kotun Jihar Katsina mai lamba 9, karkashin jagorancin Mai Shari’a I.I. Mashi, ta yanke hukuncin kisa ga mutum biyu...

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In