Wasu mutane dauke da makamai sun zo garin a kan babura kuma suka firgiJaridar SaharaReporters ta tattaro cewa yan bindigan sun isa garin ne akan babura kuma suka firgita mazauna garin wadanda basu da kariya.ta mazauna garin wadanda ba su da kariya. ‘Yan bindigar bayan sun far wa kauyen sun kwashe dabbobi suka gudu zuwa daji.
Akalla mutane 35 ne wasu ‘yan bindiga da ake zargin‘ yan fashi ne suka kashe a kauyen Sabuwar Tunga, gundumar Dankurmi da ke cikin Karamar Hukumar Maru ta Jihar Zamfara.
Wani mazaunin garin ya ce harin, wanda aka kai shi a daren Alhamis, shiri ne da aka shirya cikin tsari kuma aka hada kai.
Ya ce ‘yan bindigar bayan sun far wa kauyen sun kwashe dabbobin suka gudu zuwa daji.
“Mun gano gawarwakin sama da 35 bayan harin sannan kuma da yawa daga cikin mazauna yankin ba a san inda suke ba. Sun zo ne da tsakar dare suka bude wuta a kauyen, suna harbin kowa tare da kona gidaje, ”in ji majiyar.
Ana kai munanan hare-hare a fadin jihar ta Zamfara inda ‘yan fashi ke ci gaba da cin karensu babu babbaka.
Manoma da makiyaya a cikin jihar sun dade suna fuskantar ta’addanci daga kungiyoyin ‘yan daba wadanda ke afkawa kauyuka, satar shanu da kuma satar mazauna yankin don neman kudin fansa.
A safiyar ranar Juma’a, an sace sama da daliban makarantar sakandaren ‘yan mata ta Gwamnati 300, da ke Jangebe a karamar hukumar Talata Mafara ta jihar.
An ce ‘yan bindigar sun isa makarantar da misalin karfe 1 na dare kuma suka loda’ yan matan a cikin bas.