">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Tuesday, October 14, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Boko Haram Sun Hallaka 9, Sun Jikkata Da Dama da Bam a Tashar Mota a Borno

by Abubakar Ismail kankara
June 2, 2025
in Labarai
0
boma-boman
Share on FacebookShare on Twitter
">
">

Yayin da Boko Haram ke ci gaba da kai hare-haren kashe-kashe da rushe-rushe a yankin arewa maso gabashin Najeriya, akalla fasinjoji tara sun rasa rayukansu a kauyen Mairari, da ke ƙaramar hukumar Guzamala a Jihar Borno.

Jaridar Daily Episode ta tattaro cewa ‘yan Boko Haram sun dasa boma-boman IEDs a wajen tashar mota ta kauyen, inda boma-boman suka tarwatse suka hallaka fasinjojin da ke jiran hawa mota, lamarin da ya jikkata wasu da dama.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai, Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Borno, Abdulkarim Lawan, ya la’anci harin, yana mai bayyana shi a matsayin aikin rashin imani da takaici.

A cewarsa, “’Yan ta’addan sun riga sun mamaye gaba ɗaya ƙaramar hukumar Guzamala a halin yanzu, ko da yake ina roƙon rundunar soji da ta kawo dauki domin dawo da zaman lafiya a yankin.

“Ina cikin matuƙar bakin ciki da ɓacin rai kan rasuwar wasu mutane tara daga cikin al’ummata, waɗanda suka mutu sakamakon fashewar IED da aka dasa a kauyen Mairari. Wannan abin takaici ne ƙwarai, ina kuma roƙon Allah ya jikan su da Aljannatul Firdaus, ya kuma ba wa waɗanda suka jikkata waraka cikin gaggawa — domin a yanzu suna karɓar magani a asibitocin Monguno da Maiduguri.”

RelatedPosts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

Lawan ya ƙara da cewa, “Kauyen Mairari da abin ya faru, na ɗaya daga cikin ƙananan ƙauyuka da aka taɓa sake maido da zama a cikinsu sau biyu ta hanyar ƙoƙarin fararen hula a Guzamala, amma a yau an sake ruguza shi sakamakon dawowar hare-haren Boko Haram/ISWAP.

“Za ka ga yadda mutanen nan suke da jajircewa, domin mafi yawan waɗanda ke zaman gudun hijira a Maiduguri, Monguno da Guzamala na yawan dawowa Mairari domin kasuwanci da harkar noma.

“Amma abin takaici, a yau waɗannan ‘yan ta’adda sun yi nasarar dasa boma-boma a tashar mota ta kauyen, inda ta fashe ta hallaka mutane da dama masu laifi, tare da jikkata wasu da dama da suke fama da munanan raunuka.”

A cewarsa, “A wannan lokaci na tsaka mai wuya, yana da matuƙar muhimmanci a mayar da hankali wajen kwato Guzamala daga hannun ‘yan ta’adda. Duk da cewa mun san sabon kwamandan rundunar Operation Hadin Kai, Manjo Janar Abdulsalam Abubakar, da dakarunsa suna bakin kokarinsu wajen yaki da ‘yan ta’adda da dawo da zaman lafiya a arewa maso gabas — kwato Guzamala zai zama babban nasara da ya kamata a fifita.”

A lokacin da Daily Episode ke wallafa wannan rahoto, rundunar sojin Najeriya ba ta fitar da wata sanarwa ta hukuma ba dangane da lamarin.

">

DAILY EPISODE HAUSA

KU BIYO MU A FACEBOOK 

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

by Yahuza Bawage
October 6, 2025
0

A wasu yankuna da ke kudancin jihar Kaduna a arewacin Najeriya, mallakar fili, musamman na noma, wani abu ne da...

zaben cike gurbi

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Tun bayan kammala zaben cike gurbi da aka gudanar a fadin kasar nan, rundunar yan sandan jahar ta bayyana irin...

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Duba da yadda rashin magudadan ruwa ke sanadiyar rubtawar kabaruruka musamman a lokutan damina, al’ummar unguwar Dala da kewaye dake...

yunƙurin kashe kansa

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2025
0

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wani mutum mai shekara 50 da aka bayyana sunansa da Modu Isa ya...

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

by Abubakar Ismail kankara
August 16, 2025
0

A dai-dai lokacin da ake fama da yawan yaran da basa zuwa makaranta musamman a fadin arewacin kasar nan, mai...

Tsaro Ya Inganta

Kasa da Awa Ɗaya Bayan Ya Wallafa Cewa Tsaro Ya Inganta, ’Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shi

by Abubakar Ismail kankara
August 15, 2025
0

Rahotan da Daily Episode Hausa ta tattara daka jaridar idon mikiya na nuna da cewa, yan bindiga dake yawan kashe...

Next Post
Sallar Layya: Cinkoso Ya Rike Dubban Matafiya a Hanyar Abuja-Kano

Sallar Layya: Cinkoso Ya Rike Dubban Matafiya a Hanyar Abuja-Kano

Jami’ar Usmanu Danfodiyo

Farfesa Na Jami’ar Usmanu Danfodiyo Ya Rasu Yana Jiran Taimakon Kudin Magani

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In