">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Sunday, October 12, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Ba Zaman Sulhu Idan Har Kana Ci Gaba da Ta’addanci — Gwamnatin Sakkwato Ga Bello Turji

Idan Da Gaske Kake, Ka Saki Wadanda Ka Sace Ka Daina Hare-Hare

by Abubakar Ismail kankara
July 7, 2025
in Labarai
0
yan bindiga
Share on FacebookShare on Twitter
">

 

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta bayyana cewa ba za ta zaunawa da shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, domin tattaunawar sulhu ba, har sai ya dauki matakai na ainihi da suka hada da dakatar da hare-hare da sakin mutanen da ke hannunsa.

Kanar Ahmed Usman (mai ritaya), wanda shi ne mai ba gwamnan jihar shawara kan harkokin tsaro, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa, biyo bayan bayyanar wani faifan bidiyo da Bello Turji ya fitar, inda ya bukaci a shiga tattaunawa da shi.

Turji dai wanda aka dade ana zarginsa da jagorantar munanan hare-hare a Sakkwato da wasu jihohin makwabta, ya saki bidiyon ne kwanaki bayan jami’an tsaro sun kashe wasu daga cikin manyan kwamandojinsa sama da dari, a hadin gwiwa da jami’an tsaro na kasashen waje ciki har da Faransa.

RelatedPosts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

Kanar Ahmed ya ce babu wata hujja da ke tabbatar da cewa bukatar sulhun Bello Turji na gaskiya ne, sai dai idan ya saki duk mutanen da ke tsare a hannunsa tare da dakatar da kai farmaki a yankunan da ke fama da rikice-rikice.

“In har yana da niyyar zaman lafiya da gaskiya, to dole ne ya daina kai hare-hare a kauyuka da saki wadanda ya yi garkuwa da su ba tare da wani sharadi ba,” in ji Kanar Ahmed.

Ya kara da cewa gwamnati ba za ta lamunci duk wani yunkuri na tattaunawa yayin da jama’a ke rayuwa cikin fargaba, kuma ‘yan bindiga na ci gaba da addabar su.

A cewarsa, “Zaman lafiya na bukatar matakan gina amana daga bangarorin da abin ya shafa, ba kawai kalmomi ba.”

Kanar Ahmed ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar ta kuduri aniyar samar da tsaro da kwanciyar hankali, kuma ba za ta lamunci ta’addanci da sauran laifuka ba.

A karshe, ya bukaci hadin kan al’umma, shugabannin gargajiya, malamai da kungiyoyin fararen hula wajen marawa gwamnati baya domin dorewar zaman lafiya a jihar.

">
">

DAILY EPISODE HAUSA

KU BIYO MU A FACEBOOK

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

by Yahuza Bawage
October 6, 2025
0

A wasu yankuna da ke kudancin jihar Kaduna a arewacin Najeriya, mallakar fili, musamman na noma, wani abu ne da...

zaben cike gurbi

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Tun bayan kammala zaben cike gurbi da aka gudanar a fadin kasar nan, rundunar yan sandan jahar ta bayyana irin...

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Duba da yadda rashin magudadan ruwa ke sanadiyar rubtawar kabaruruka musamman a lokutan damina, al’ummar unguwar Dala da kewaye dake...

yunƙurin kashe kansa

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2025
0

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wani mutum mai shekara 50 da aka bayyana sunansa da Modu Isa ya...

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

by Abubakar Ismail kankara
August 16, 2025
0

A dai-dai lokacin da ake fama da yawan yaran da basa zuwa makaranta musamman a fadin arewacin kasar nan, mai...

Tsaro Ya Inganta

Kasa da Awa Ɗaya Bayan Ya Wallafa Cewa Tsaro Ya Inganta, ’Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shi

by Abubakar Ismail kankara
August 15, 2025
0

Rahotan da Daily Episode Hausa ta tattara daka jaridar idon mikiya na nuna da cewa, yan bindiga dake yawan kashe...

Next Post
fasahar ƙirƙirar basira

AI na Barazana Ga Ayyuka Sama da Miliyan 92 a Duniya — Farfesa Umaru Pate

Fursunoni

Fursunoni 58 Sun Rubuta Jarabawar NECO A Gidan Yarin Kano

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In