">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Wednesday, October 15, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

An Zargi Jami’an C-Watch Da Harbin Mutane Sama Da 30 a Garin Mabai, Jahar Katsina

by Abubakar Ismail kankara
June 11, 2025
in Labaran Ketare
0
Jami’an C-Watch
Share on FacebookShare on Twitter
">

Wasu daga cikin jami’an Katsina Community Watch Corps (C-Watch) sunyi harbin uwa da wabi da harsasai a Mabai, karamar hukumar Kankara ta jihar Katsina, inda suka bar mutane fiye da 30 da raunuka, da jinya mai tsanani a asibitocin Katsina, Kankara da Malumfashi.

Lamarin ya fara ne lokacin da wasu daga cikin jami’an C-Watch din suka nemi yima wa wani matashi mai suna Mutaka Adamu wanda aka fi sani da Bamba, aski sakamoakn ya tara suma yayin bukukuwan Sallah a garin Mabai ranar Litinin, 9 ga Yuni, 2025.

A cewar wanda abun ya faru a gaban sa mai suna Aliyu Usman Mabai, “jami’an sun tare Bamba suka ce dole sai sun aske masa gashin kansa bisa dalilin da suka bayyana a matsayin wani bangare na dokar kula da aka basu. Amma matashin ya ki yarda, inda ya baiyana masu cewa bai aikata wani laifi ba.”

RelatedPosts

Kotu a Najeriya ta yanke wa Yan China 9 hukuncin dauri kan laifin damfara da ta’addanci

Ƴan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Aikata Laifuka Da Makamai Bayan Kisan Soja a Kaduna

Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 37 A Jamhuriyar Nijar

Mun Yafema Kowa – Cewar Kungiyar Taliban

 

Ya ci gaba da cewa, “Wasu dattawa a yankin sun shiga tsakani, inda suka roki jami’an su bar Bamba saboda tara suma ba laifi ba ne a shari’ar Musulunci ko al’ada.”

Bayan lokaci kadan, jami’an suka dawo suka kama Bamba a wata makarantar firamare. “ inda sukayi masa duka har sai da ya fita hayacinsa. ” in ji Aliyu.

Bayan al’ummar yankin sun ji yadda aka daka Bamba, matasa da dama suka fusata, suna tambayar dalilin da ya sa aka yi masa haka.

Daka bisani sai matasa suka fara cewa bamu yard aba inda har suka fara yima jami’an ihu suna cewa “bamayi, bamayi”.

Sai kawai jami’an suka bude wuta, inda suka harbi mutane da dama ciki har da mata da yara, wasu ma suna cikin gidajensu lokacin harbin.

Sojojin da ke zaune a Mabai ne suka zo inda daka bisani suka kwantar da tarzoma tare da taimaka wa wajen daukar masu rauni zuwa Asibitin Gwamnati na Kankara. Inda daka bisani aka kai wasu asbitin a katsina, malunfashi da kuma bakori sakamokon munin raunin da suka ji.

Alhaji Adamu Mamman, mahaifin Bamba, ya bayyana cewa lamarin abin bakin ciki ne. “A lokacin da muke fama da rashin tsaro, ba dace irin wannan abu ya faru ba. A daidai wannan lokaci, ya kamata a mayar da hankali wajen yaki da ‘yan ta’adda da barayin daji.”

">

Ya ci gaba da cewa, “Jami’an C-Watch sun so hana bikin Sallah da ake yi duk shekara a unguwarmu. Amma matasa suka ki amincewa. Sai suka ce wai dakarun soja sun ce kada a yi bikin. Daga nan ne suka fara neman Bamba da sharri.”

">

“Muna cikin damuwa da wadanda ke kwance a asibiti, musamman masu raunuka masu tsanani. Ko da yake mun samu labarin cewa an kama jami’an kuma an mika su ga ‘yan sanda, amma muna kira da a gudanar da bincike mai kyau da sulhu don zaman lafiya,” in ji shi.

DAILY EPISODE HAUSA

KU BIYO MU A FACEBOOK 

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Kotu a Najeriya ta yanke wa Yan China 9 hukuncin dauri kan laifin damfara da ta’addanci

Kotu a Najeriya ta yanke wa Yan China 9 hukuncin dauri kan laifin damfara da ta’addanci

by Abubakar Ismail kankara
June 10, 2025
0

Lagos, Najeriya — Babbar Kotun Tarayya da ke Ikoyi, jihar Lagos, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a D.E. Osiagor, ta yanke wa...

Ƴan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Aikata Laifuka Da Makamai Bayan Kisan Soja a Kaduna

Ƴan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Aikata Laifuka Da Makamai Bayan Kisan Soja a Kaduna

by Abubakar Ismail kankara
June 10, 2025
0

Jami’an ƴan sanda a Jihar Kaduna sun tabbatar da kama mutane 13 da ake zargi da hannu a kisan wani...

An harbe ‘Yan Bindiga Yayinda Sukaje Karbar Kudin Fansa

Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 37 A Jamhuriyar Nijar

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2021
0

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na cewa wasu mahara sun kashe mutum 37 a kauyen Darey Dey da ke yankin Banibangou...

Mun Yafema Kowa – Cewar Kungiyar Taliban

Mun Yafema Kowa – Cewar Kungiyar Taliban

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2021
0

Kungiyar Taliban ta bayyana cewa za ta tabbatar kowanne dan kasar Afghanistan ya samu damar walwala tana mai cewa ba...

Auren Attajirin Duniya Bill Gates Da Matarsa Melinda Ya Rabu

Auren Attajirin Duniya Bill Gates Da Matarsa Melinda Ya Rabu

by Maryam Umar Said
August 5, 2021
0

Rahotanni daga kasar Amurka na bayyana cewar Auren mashahurin mai kudin nan na duniya Bill Gates da matarsa Melinda French...

Jamhuriyar Nijar Ta Cika Shekara 61 Da Samun ’Yanci

Jamhuriyar Nijar Ta Cika Shekara 61 Da Samun ’Yanci

by Maryam Umar Said
August 4, 2021
0

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya taya takwaransa na Jamhuriyar Nijar, Mohammed Bazoum, murnar zagayowar ranar samun ’yancin kan kasar...

Next Post
Yan Uwan Yan Darikar Tijjaniyya 13 da Akayi Garkuwa Dasu a Burkina Faso Sun Roki Shugaba Tinubu da Gwamna Yusuf su Taimaka

Yan Uwan Yan Darikar Tijjaniyya 13 da Akayi Garkuwa Dasu a Burkina Faso Sun Roki Shugaba Tinubu da Gwamna Yusuf su Taimaka

ƙasurguman ‘yan ta’adda

Sojojin Nijeriya Sun Kashe Auta Da Wasu Manyan ’Yan Ta’adda a Zamfara

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In