">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Wednesday, October 15, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

An buƙaci ‘yan Kano da Jigawa da ke kewayen Tiga Dam da su tashi saboda fargabar ambaliyar ruwa

by Abubakar Ismail kankara
July 25, 2025
in Labarai
0
ambaliya
Share on FacebookShare on Twitter
">
">

Biyo bayan hasashen da Hukumar Yanayi ta Ƙasa (NiMet) da Hukumar Kula da Ruwa ta Ƙasa (NIHSA) suka fitar, wanda ke nuna cewa wasu al’ummomi a sassa daban-daban na ƙasar na fuskantar barazanar ambaliya, manajan Dam ɗin Tiga, Alhaji Abdulkadir Salisu, ya yi kira ga manoma da mazauna yankunan da ambaliya ke yawan afkuwa da su bi matakan kariya tare da shiryawa domin ficewa daga yankunan kafin lokaci ya kure.

A wata tattaunawa da Jaridar Daily Episode, Salisu ya karyata zargin cewa ambaliyar da ta mamaye wasu kauyuka a Kano da Jigawa sakamakon sakin ruwa ne daga Dam ɗin Tiga.

A cewarsa:

“Wannan ambaliya da mutane ke fuskanta a halin yanzu ruwa ne daga ruwan sama mai karfi — ba daga Dam ɗin Tiga ba. Saboda dam din Tiga yakan fara sakin ruwa ne daga watan Agusta zuwa Satumba.”

Ya kara da cewa akwai tsarin da suka tanada wanda ke bai wa jama’a, musamman shugabannin al’umma kamar hakimai da dagatai, bayani game da matakin ruwa a Dam, domin a shirya tun kafin matsala ta faru.

RelatedPosts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

“Wasu mutane suna komawa gidajensu da wuri bayan ruwa ya lafa, alhali hakan ba daidai ba ne. Yakamata a bar yankunan da ambaliya ke barazana tuni, domin ruwan sama na kara taruwa a rafuka da koguna, wanda ke haddasa kwararar ruwa cikin al’umma da ke jawo ruɗani cewa dak Dam ne ake sakin ruwan.”

Alhaji Salisu ya bukaci mazauna yankunan kogin da sauran wuraren da aka san suna fuskantar ambaliya da su fara shirin ficewa tun yanzu, duba da cewa watan Agusta na ƙaratowa.

“Ko da yake ba za mu iya dakatar da abubuwan da suka shafi halitta ba, musamman ma idan sun faru cikin dare, amma matakan kariya sun fi muhimmanci. Yakamata kowa da kowa da ke zaune a kusa da koguna ya dauki matakin gaggawa kafin abin ya lalace.”

DAILY EPISODE HAUSA

">

KU BIYO MU A FACEBOOK

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

by Yahuza Bawage
October 6, 2025
0

A wasu yankuna da ke kudancin jihar Kaduna a arewacin Najeriya, mallakar fili, musamman na noma, wani abu ne da...

zaben cike gurbi

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Tun bayan kammala zaben cike gurbi da aka gudanar a fadin kasar nan, rundunar yan sandan jahar ta bayyana irin...

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Duba da yadda rashin magudadan ruwa ke sanadiyar rubtawar kabaruruka musamman a lokutan damina, al’ummar unguwar Dala da kewaye dake...

yunƙurin kashe kansa

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2025
0

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wani mutum mai shekara 50 da aka bayyana sunansa da Modu Isa ya...

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

by Abubakar Ismail kankara
August 16, 2025
0

A dai-dai lokacin da ake fama da yawan yaran da basa zuwa makaranta musamman a fadin arewacin kasar nan, mai...

Tsaro Ya Inganta

Kasa da Awa Ɗaya Bayan Ya Wallafa Cewa Tsaro Ya Inganta, ’Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shi

by Abubakar Ismail kankara
August 15, 2025
0

Rahotan da Daily Episode Hausa ta tattara daka jaridar idon mikiya na nuna da cewa, yan bindiga dake yawan kashe...

Next Post
cutar gastroschisis

Ana Neman Tallafin Jama'a Domin Ceto Jariri da Aka Haifa da Cutar Gastroschisis a Jigawa

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wadanda Suka Kashe Tsohon Kwamishina a Katsina

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wadanda Suka Kashe Tsohon Kwamishina a Katsina

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In