">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Friday, October 10, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Biden da Netanyahu sun tattauna kan tsagaita wuta a Gaza

by Abubakar Ismail kankara
January 13, 2025
in Sport Stories
0
Biden da Netanyahu sun tattauna kan tsagaita wuta a Gaza
Share on FacebookShare on Twitter
">

RelatedPosts

Gobarar Tankar Fetur Ta Yi Ajalin Mutane da Dama a Neja

Iyalan Waɗanda Harin Sojoji ya Shafa a Zamfara Sun Nemi Diyya da Tallafi

Kananan Hukumomi Za Su Fara Karɓar Kuɗaɗensu Kai Tsaye – Fadar Shugaban Ƙasa

Kano Ta Dauki Matakan Gaggawa Kan Rahoton Cutar Murar Tsuntsaye

Shugaban Amurka, Joe Biden da Firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu sun tattauna ta waya a daidai lokacin da ake ci gaba da zura ido dangane da batun tsagaita wutar Gaza – a makon ƙarshe na Biden a matsayin shugaban Amurka.

">
">

Alamu na nuna cewa Isra’ila da Hamas sun fahimci juna kuma suna ci gaba da tattaunawa duk da cewa akwai ƴan abubuwan da suka ƙi yarda da juna a kai.

Fadar White House ta ce Biden ya tattauna kan “muhimman abubuwan da za su iya sauya yanayin da Gabas Ta Tsakiya ke ciki” tun bayan tsagaita wuta da Hezbollah a Lebanon, da faɗuwar gwamnatin Assad a Syria da kuma gurgunta ƙarfin Iran a yankin na Gabas ta Tsakiya.

Ofishin firaiminista Netanyahu ya ce ya sanar da Biden kan umarnin da ya bayar ga manyan masu shiga tsakani a Doha “domin su tabbatar da sakin mutanen da ake garkuwa da su”.

Shugaban Amurka, Joe Biden da Firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu sun tattauna ta waya a daidai lokacin da ake ci gaba da zura ido dangane da batun tsagaita wutar Gaza – a makon ƙarshe na Biden a matsayin shugaban Amurka.

Alamu na nuna cewa Isra’ila da Hamas sun fahimci juna kuma suna ci gaba da tattaunawa duk da cewa akwai ƴan abubuwan da suka ƙi yarda da juna a kai.

Fadar White House ta ce Biden ya tattauna kan “muhimman abubuwan da za su iya sauya yanayin da Gabas Ta Tsakiya ke ciki” tun bayan tsagaita wuta da Hezbollah a Lebanon, da faɗuwar gwamnatin Assad a Syria da kuma gurgunta ƙarfin Iran a yankin na Gabas ta Tsakiya.

Ofishin firaiminista Netanyahu ya ce ya sanar da Biden kan umarnin da ya bayar ga manyan masu shiga tsakani a Doha “domin su tabbatar da sakin mutanen da ake garkuwa da su”.

Yayin wata tattaunawa ta waya wanda ita ce irinta ta farko da aka bayyana tun watan Oktoba, Biden “ya nanata bukatar gaggawa ta kammala yarjejeniyar tsagaita wutar ta Gaza da kuma sakin mutanen da aka yi garkuwa da su da kuma ƙara yawan kayan jin ƙai”.

Wannan dai na zuwa ne kwana guda bayan da Netanyahu ya aike da babbar tawagar jami’an tsaron Isra’ila da suka haɗa da daraktocin ƙunigyar leƙen asiri ta Mossad da tsaron ƙasar, Shin Bet domin wucewa gaba a cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da Qatar da AMurka da Misra ke jagoranta.

Kafafen watsa labaran Isra’ila sun rawaito cewa Netanyahu ya gana da jami’an gwamnatinsa da ke adawa da shirin tsagaita wutar domin ya lallaɓe su ka da su yi murabus.

Ministan harkokin wajen Burtaniya, David Lammy ya gana da Benjamin Netanyahu a Jerussalem domin tattauna cigaban da ake samu dangane da yarjejeniyar.

A ranar A sabar ne wakili na musamman da zaɓaɓɓen shugaban Amurka, Donald Trump a Gabas ta Tsakiya ya gana da Benjamin Netanyahu kan yarjejeniyar kafin ranar 20 ga watan Janairu – ranar da za a rantsar da Trump ɗin.

A baya dai mista Trump ya ce “za a yi ɓatacciya” idan dai har ba a saki waɗanda ake garkuwar da su ba kafin ya sake kama aiki.

A ranar Alhmis ɗin da ta gabata ne sakataren harkokin wajen Amurka, Anthony Blinken ya ce “yarjejeniyar na dab” da kasancewa kamar yadda muke fata kafin Trump ya kama aiki. Duk wata yarjejeniya da za a cimma to za ta zama bisa doron tsarin da Joe Biden ya shaimfiɗa.

Duk da cewa ana aiki tuƙuru kan yarjejeniyar, amma rashin cikakken bayani kan wasu muhimman abubuwa da suka haɗa da ko yarjejeniyar ta farko za ta ɗore zuwa tsayar da yaƙin baki ɗaya sannan ko Isra’ila za ta amince da janye sojojinta daga Gaza baki ɗaya.

Sai dai kuma wakilin jaridar Isra’ila ta The Economist, Anshel Pfeffer ya ce ba ya tsammanin za a iya cimma wata yarjejeniya cikin gaggawa.

To amma ya ƙara da cewa burin Isra’ila da Hamas ne ganin sun cimma yarjejeniyar kafin Trump ya kama mulki.

“Akwai fargaba tare da Hamas cewa Trump ka iya bai wa Netanyahu damar ƙaddamar da muggan hare-haren da a baya ba su yi ba.”

“Dukkan ɓangarorin sun nuna gajiya, sun wahala sosai.”

Isra’ila ta ce har yanzu dai akwai ragowar waɗanda Hamas ke garkuwa da su a Gaza su 94, kuma ana tsammanin 34 daga ciki sun rasu tare da ƙarin mutum huɗu da Hamas ɗin ta kama gabanin yaƙin inda biyu daga cikinsu suka mutu.

DAILY EPISODE HAUSA

KU BIYO MU A FACEBOOK DA X

Source: BBC Hausa
Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Gobarar Tankar Fetur

Gobarar Tankar Fetur Ta Yi Ajalin Mutane da Dama a Neja

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Mutane da dama, ciki har da wata mai juna biyu, sun rasu yayin da gobara ta tashi lokacin da suke...

harin jiragen Sojin

Iyalan Waɗanda Harin Sojoji ya Shafa a Zamfara Sun Nemi Diyya da Tallafi

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Iyalan waɗanda harin jiragen Sojin saman Najeriya ya rutsa da su a Zamfara sun nemi gwamnati ta biya su diyya...

Asusun Bai Ɗaya

Kananan Hukumomi Za Su Fara Karɓar Kuɗaɗensu Kai Tsaye – Fadar Shugaban Ƙasa

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Fadar shugaban ƙasa ta sanar da cewa, daga ƙarshen watan Janairu, dukkan kananan hukumomi a Najeriya za su fara karɓar...

Murar Tsuntsaye

Kano Ta Dauki Matakan Gaggawa Kan Rahoton Cutar Murar Tsuntsaye

by Abubakar Ismail kankara
January 17, 2025
0

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta yi kira ga al’umma da su kwantar da hankali tare da kai rahoton duk...

rikicin masarautar Kano

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Umarci Sake Sauraron Shari’ar Rikicin Masarautar Kano

by Abubakar Ismail kankara
January 10, 2025
0

Kotun ɗaukaka ƙara da ke Abuja ta bayar da umarnin sake sauraron shari’ar rikicin masarautar Kano da ya haɗa da...

Katsina Zuwa Jibia

Hanyar Katsina Zuwa Jibia Tana Buƙatar Taimakon Gaugawa …

by Abubakar Ismail kankara
January 9, 2025
0

Daga: Muhammad Aminu Kabir Matafiya akan hanyar Katsina zuwa Jibia na cigaba da kokawa akan rashin kyawon hanya musamman a...

Next Post
Hukumar Tattara Haraji

EFCC Ta Kama Jami’an Haraji 5 Kan Satar Biliyan 1.2 a Katsina

Murar Tsuntsaye

Kano Ta Dauki Matakan Gaggawa Kan Rahoton Cutar Murar Tsuntsaye

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In