">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Wednesday, October 15, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

An kama matar da ake zargi da kai wa Bello Turji makamai daji a Zamfara

by Abubakar Ismail kankara
December 30, 2024
in Technologies
0
An kama matar da ake zargi da kai wa Bello Turji makamai daji a Zamfara
Share on FacebookShare on Twitter
">

RelatedPosts

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 6 a Sakkwato

An Kashe Shahararren Dan Ta’adda Gwaska, Yayin Da Mazauna Yakin Yantumaki Ke Hijira Kan Tarar N30m Da Barazanar Kisa

Shugaba Buhari Ya Bukaci Shugabannin Tsaro Su Kawo Sabbin Dabaru Kan Tsaron Kasar Nan

Ýan Bindiga Sun Kai Sabon Harin Da Suka Yi Garkuwa Da Mutane 18 A Kaduna

">
">

Bataliyar rundunar sojin Najeriya mai yaƙi da yan fashin daji a arewa maso yammacin Najeriya da ake kira da Operation Fansar Yamma, ta samu nasarar cafke wata mata mai shekaru 25 da haihuwa dauke da alburusai 764 da kuma bindigogi guda shida, da ake zargin za ta kai sansanin madugun ƴan fashin dajin nan Bello urji

Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar laftanal kanal Abubakar Abdullahi ya fitar, ya ce an kama matar ne a ranar 28 ga watan Disamban 2024 da ake ciki, tare da wani abokin tafiyarta a yankin Badarawa da ke karamar hukumar Shinkafi ta jihar Zamfara.

Kamen dai ya biyo bayan wani rahoton sirri da aka samu game da safarar makaman ƴan bindigar a kan hanyar Kware zuwa Badarawa a karamar hukumar ta Shinkafi.

Bayan samun waɗannan bayanai ne dakarun rundunar ta Operation Fansar Yamma suka kafa wani shingen bincike wanda ya kai ga cafke wadanda ake zargin.

A halin yanzu dai ana ci gaba da bincikar mutanen da aka kama.

Sanarwar ta ƙara da cewa rundunar ta ƙuduri aniyar ci gaba da daukar dukkan matakan da suka kamata domin daƙile safarar makamai ga ƴan bindigar, da ke ci gaba da tayar da zaune tsaye a yankin.

Don haka ta yi kira ga jama’a da kada su gajiya wajen bayar da sahihan bayanan da za su kai ga samun wannan nasara, da ma kamo su kansu ƴan bindigar da aka jima ana nema ruwa a jallo.

Dama dai an jima ana zargin akwai masu kai wa ƴan bindigar makaman da suke amfani da su har dazukan da suke a wannan yanki musamman ita Zamfara, da ta fi fama da wannan matsala.

Ko a watan Nuwamban da ya gabata ma sai da rundunar ƴan Sandan Jihar ta kama wani ɗan ƙasar Aljeriya, mai shekaru 58 kan zargin safarar makamai daga wasu ƙasashe maƙwabtan Najeriya inda ya ke shiga da su ta Zamfara.

A wannan lokaci kwamishinan ƴan sandan jihar Mohammed Dalijan, ya faɗawa BBC Hausa cewa sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda 16, yayin samame daban-daban da suka kai cikin makonni uku da suka gabata sakamakon bayanan sirrin da suka samu daga shi wannan mutumi.

Kana ya bayar da bayanan wasu mutanen suma da suke samar da makaman a Jos, jihar Plateau, da suma ake safararsu zuwa yanki.

Hakazalika, sun samu wasu manyann bindigogi guda biyu da wata bindiga ƙirar gida daga hannun wani mai ƙera makamai a Jos, Jihar Filato.

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

hallaka ’yan ta’adda

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 6 a Sakkwato

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Sojojin rundunar Operation Hadarin Daji sun hallaka ’yan ta’adda shida a wani artabu da ya faru a karamar hukumar Gudu,...

yan bindiga

An Kashe Shahararren Dan Ta’adda Gwaska, Yayin Da Mazauna Yakin Yantumaki Ke Hijira Kan Tarar N30m Da Barazanar Kisa

by Abubakar Ismail kankara
February 11, 2022
0

Sama da mutane dubu daya mazauna kauyen Tashar Biri suka tsere daga kauyen da ke Yatumaki a karamar hukumar Dan...

Buhari Ya Nemi Shugabannin Tsaro Su Kawo Sabbin Dabaru Kan Tsaro

Shugaba Buhari Ya Bukaci Shugabannin Tsaro Su Kawo Sabbin Dabaru Kan Tsaron Kasar Nan

by Maryam Umar Said
September 8, 2021
0

A zaman da ya wakana a jiya Talata a fadar shugaban kasa kan yanayin tsaron kasar nan, shugaba Buhari ya...

Ýan Bindiga Sun Kai Sabon Harin Da Suka Yi Garkuwa Da Mutane 18 A Kaduna

Ýan Bindiga Sun Kai Sabon Harin Da Suka Yi Garkuwa Da Mutane 18 A Kaduna

by Maryam Umar Said
September 7, 2021
0

Ýan bindiga sun kai sabon hari a unguwar Keke da ke Karamar Hukumar Chikun ta Jihar Kaduna. Ýan bindigar sun...

Munyi Rashin Ýan Wasa Amma Hakan Bazai Kawo Mana Naqasu Ba – Ahmad Musa

Munyi Rashin Ýan Wasa Amma Hakan Bazai Kawo Mana Naqasu Ba – Ahmad Musa

by Maryam Umar Said
September 7, 2021
0

Canja shekar da wasu daga cikin ýan wasan kungiyar kwallon kafa ta kasa Super Eagle sukayi bazai kawo naqasu a...

Aikin Ýan Bindiga Bai Shafi Yare Ko Addini Ba – El-Rufa’i

Aikin Ýan Bindiga Bai Shafi Yare Ko Addini Ba – El-Rufa’i

by Maryam Umar Said
August 30, 2021
0

Riqaqqun ýan ta'addan da aka fi sani da Ýan bindiga, wadanda suka yi kaurin suna wajen satar shanu, garkuwa da...

Next Post
Sanata Barau ya tura matasa 70 karatu kasar India

Sanata Barau ya tura matasa 70 karatu kasar India

Hukumar Hisbah Ta Fara Kauda Yara Masu Gara-Ranba Daga Titunan Kano

Hukumar Hisbah Ta Fara Kauda Yara Masu Gara-Ranba Daga Titunan Kano

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In