">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Wednesday, October 15, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Sojoji Sun Kashe Yan Bindiga 20 Dasukayi Yunkurin Kai Hari NDA

by Abubakar Ismail kankara
February 13, 2022
in Labarai
0
yan fashi da garkuwa da mutane
Share on FacebookShare on Twitter
">

Yayin da arewacin Najeriya ke fama da karuwar ta’adancin ‘yan fashi da garkuwa da mutane, rundunar sojin saman Najeriya ta dakile harin da wasu ‘yan ta’adda na ‘yan bindiga suka kai a makarantar horas da sojoji ta Najeriya wato NDA

A cewar wani rahoto da kafar yada labarai ta PR Nigeria ta wallafa, an kawar da ‘yan ta’adda kusan 20 a ranar Alhamis yayin da suke tserewa domin gujewa harin bama baman sojojin saman Najeriya.

Rahotanni sun ce ‘yan ta’addan sun tunkari cibiyar horas da sojoji kimanin su 50 a kan babura tare da shirin sake kai harin da suka samu nasara a bara.

Ku tuna cewa Daily Episode ta ruwaito yadda ‘yan bindiga suka kai hari makarantar horas da sojoji ta Najeriya, NDA, kuma suka yi garkuwa da wasu jami’an soji tare da kashe wasu.

RelatedPosts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

Jihar Kaduna dai ta kusa tabarbare a fannin tsaro a ‘yan kwanakin nan ganin yadda yankunan Arewa, Gabas, Yamma, da Kudancin jihar ke fama da tashe-tashen hankula a harkokin tsaro tare da yawaitar sace-sacen mutane, kashe-kashe, satar shanu, da rikicin addini da na kabilanci.

Wani Bakon Kisan Da Aka Yi Wa Manajan Kaduna

Hankalin Jama’a ya tashi a jahar Kaduna ranar Juma’a, yayin da aka kashe wani babban ma’aikaci mai mukamin Darakta ayyuka na Kaduna Geographic Information Service (KADGIS), a gidansa mai iyaka da sansanin sojojin saman Najeriya da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna.

Late. Dauda Aliyu Anchau,

Daily Episode ta tattaro cewa wasu makasa sun samu shiga gidan marigayin da ke Barakallahu GRA, karamar hukumar Igabi, jihar Kaduna, domin aiwatar da kisan.

">

Alhaji Ibrahim Gaya, mazaunin unguwar kuma shugaban al’ummar garin Barakallahu GRA, ya bayyana kaduwarsa da faruwar lamarin, inda ya koka da cewa duk da kokarin da suke yi wajen tabbatar da tsaro a unguwarsu da muhallinsu, anma wasu mahara sun karya yunkurinsu na kashe wani mutum mai muhimmanci, wanda ya amfanar da al’umma da jihar kaduna.

Muna fatan jami’an tsaro za su gano wadanda suka aikata wannan kisan gilla domin ba a sace kowa ba, ba a kuma sace dukiya ba; masu laifin kawai sunzo ne don su dauki ran Dauda ne kawai.

Sai dai ya bukaci gwamnatocin tarayya da na jihohi da su kara inganta tsaro a kasar nan, musamman na kananan hukumomin Igabi da Giwa, da ke kara samun karuwar laifukan da suka shafi ‘yan fashi, yan bindiga da masu garkuwa da mutane.

Sai dai an binne marigayin ne a mahaifarsa, Anchau, kamar yadda shari’ar Musulunci ta tanada.

Maharan sun kuma yi hanyarsu ta zuwa tsohon barakallahu, inda suka afka wani gida na wani Bitrus Gajere, suka yi awon gaba da wasu kayayyaki masu daraja.

Fira da wadanda iftila’in ya afkamawa

">

Mista Bitrus ya bayyana cewa masu barayin sun harba bindiga sau biyu a cikin gidansa, suka fasa dakin dansa kuma suka sace wayoyi, kwamfutar tafi-da-gidanka, da kuma jakar dansa.

Mun gode wa Allah da babu wanda aka jikkata ko aka yi garkuwa shi, amma mun firgita kuma mun yi hasarar dukiya sakamakon abin da suka dauka.

Patience Joel ta ba da labarin yadda suka boye sa’ad da suka ji ƴan ta’addan na ƙoƙarin yin kutse da shiga ɗakinsu ta taga.

addu’a mukayi kuma muka ɓuya a wurare daban-daban. Mun jin su a lokacin da suka shigo, amma ba su same mu ba, sai suka kwashe abin da suke so.

Ba mu iya barci ba saboda harbin bindigar ya yi nauyi tareda tsorata mu.

Patience ta kuma yi kira ga gwamnati da ta taimaka wajen samar da tsaro ga al’ummarsu domin kare rayukan su da dukiyoyinsu.

Yayin da ake hada wannan rahoto, hukumomin ‘yan sanda ba su tabbatar da faruwar lamarin ba.

DAILY EPISODE HAUSA

LIKE & FOLLOW US ON FACEBOOK & TWITTER

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

by Yahuza Bawage
October 6, 2025
0

A wasu yankuna da ke kudancin jihar Kaduna a arewacin Najeriya, mallakar fili, musamman na noma, wani abu ne da...

zaben cike gurbi

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Tun bayan kammala zaben cike gurbi da aka gudanar a fadin kasar nan, rundunar yan sandan jahar ta bayyana irin...

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Duba da yadda rashin magudadan ruwa ke sanadiyar rubtawar kabaruruka musamman a lokutan damina, al’ummar unguwar Dala da kewaye dake...

yunƙurin kashe kansa

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2025
0

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wani mutum mai shekara 50 da aka bayyana sunansa da Modu Isa ya...

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

by Abubakar Ismail kankara
August 16, 2025
0

A dai-dai lokacin da ake fama da yawan yaran da basa zuwa makaranta musamman a fadin arewacin kasar nan, mai...

Tsaro Ya Inganta

Kasa da Awa Ɗaya Bayan Ya Wallafa Cewa Tsaro Ya Inganta, ’Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shi

by Abubakar Ismail kankara
August 15, 2025
0

Rahotan da Daily Episode Hausa ta tattara daka jaridar idon mikiya na nuna da cewa, yan bindiga dake yawan kashe...

Next Post
DCP Abba Kyari

Bayani dalla-dalla na yanda Abba kyari ya shiga hannu

zaben 2023

2023: Hon J.Man Ya Ayana Kudurin Takarar Majalisa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In