">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Thursday, October 16, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Muna Da Rahotannin Sirri Na Masu Ɗaukar Nauyin ‘Yan Bindiga – Fadar Shugaban Kasa

by Abubakar Ismail kankara
March 3, 2021
in Technologies
1
Muna Da Rahotannin Sirri Na Masu Ɗaukar Nauyin ‘Yan Bindiga – Fadar Shugaban Kasa
Share on FacebookShare on Twitter
">

Fadar Shugaban kasa ta bayyana cewar akwai rahotanni da bayanan sirri da take dasu dangane da masu ɗaukar nauyin ‘yan Bindiga a Najeriya musamman yankin Arewacin kasar, kuma nan gaba ba da dadewa ba za ta fallasa su.

Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Babagana Monguno ya tabbatar da hakan, inda ya ce wasu mutane suna amfani da damar tabarbarewar yanayin tsaro a kasar don amfanar kansu da kansu domin cimma manufofin su na son zuciya.

Da yake magana a ranar Talata bayan taron majalisar tsaron kasa da Shugaba Muhammadu Buhari ya jagoranta, Monguno ya ce gwamnati ba za ta lamunci lamarin ba. Ya gargadi duk wadanda ke tayar da kayar baya da su daina ko kuma su fuskanci fushin hukuma.

“Tabbas, har yanzu shugaban kasa yana ci gaba da nuna damuwa game da matakin tsaro, wanda ake ganin yana neman zama mummunan aiki, kuma da yardar Allah komai zai daidaita.

RelatedPosts

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 6 a Sakkwato

An kama matar da ake zargi da kai wa Bello Turji makamai daji a Zamfara

An Kashe Shahararren Dan Ta’adda Gwaska, Yayin Da Mazauna Yakin Yantumaki Ke Hijira Kan Tarar N30m Da Barazanar Kisa

Shugaba Buhari Ya Bukaci Shugabannin Tsaro Su Kawo Sabbin Dabaru Kan Tsaron Kasar Nan

“Ganin cewa muna da sabuwar kungiya tare da sabbin shugabannin hafsoshin tsaro, shugaban kasa ya bukaci dukkanmu da mu rubanya kokarinmu, musamman ganin abubuwan da suka faru makonni biyu da suka gabata,” in ji Monguno.

“Yanzu, ina bukatar in kara jaddada cewa akwai wasu mutane a kasar nan wadanda suka dauki matsayin da ya wuce abin da ya kamata su zama. “Bayanan da muke samu daga majiyarmu, bayanan da nake dasu da kuma na sauran bayanan sirri, sun nuna cewa muna da wasu kungiyoyi, na wasu mutane da suke cin gajiya saboda rashin tsaro, musamman satar mutane.”

Ya kuma gargadi wadanda ba ‘yan jiha ba da ke haifar da matsaloli a sassa daban-daban na kasar nan da su daina yin hakan, ya kara da cewa hukumomin leken asiri sun sanya musu ido, kuma za suyi maganin su.

">

DAILY EPISODE HAUSA

">

KU BIYO MU A FACEBOOK DA TWITTER

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

hallaka ’yan ta’adda

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 6 a Sakkwato

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Sojojin rundunar Operation Hadarin Daji sun hallaka ’yan ta’adda shida a wani artabu da ya faru a karamar hukumar Gudu,...

An kama matar da ake zargi da kai wa Bello Turji makamai daji a Zamfara

An kama matar da ake zargi da kai wa Bello Turji makamai daji a Zamfara

by Abubakar Ismail kankara
December 30, 2024
0

Bataliyar rundunar sojin Najeriya mai yaƙi da yan fashin daji a arewa maso yammacin Najeriya da ake kira da Operation...

yan bindiga

An Kashe Shahararren Dan Ta’adda Gwaska, Yayin Da Mazauna Yakin Yantumaki Ke Hijira Kan Tarar N30m Da Barazanar Kisa

by Abubakar Ismail kankara
February 11, 2022
0

Sama da mutane dubu daya mazauna kauyen Tashar Biri suka tsere daga kauyen da ke Yatumaki a karamar hukumar Dan...

Buhari Ya Nemi Shugabannin Tsaro Su Kawo Sabbin Dabaru Kan Tsaro

Shugaba Buhari Ya Bukaci Shugabannin Tsaro Su Kawo Sabbin Dabaru Kan Tsaron Kasar Nan

by Maryam Umar Said
September 8, 2021
0

A zaman da ya wakana a jiya Talata a fadar shugaban kasa kan yanayin tsaron kasar nan, shugaba Buhari ya...

Ýan Bindiga Sun Kai Sabon Harin Da Suka Yi Garkuwa Da Mutane 18 A Kaduna

Ýan Bindiga Sun Kai Sabon Harin Da Suka Yi Garkuwa Da Mutane 18 A Kaduna

by Maryam Umar Said
September 7, 2021
0

Ýan bindiga sun kai sabon hari a unguwar Keke da ke Karamar Hukumar Chikun ta Jihar Kaduna. Ýan bindigar sun...

Munyi Rashin Ýan Wasa Amma Hakan Bazai Kawo Mana Naqasu Ba – Ahmad Musa

Munyi Rashin Ýan Wasa Amma Hakan Bazai Kawo Mana Naqasu Ba – Ahmad Musa

by Maryam Umar Said
September 7, 2021
0

Canja shekar da wasu daga cikin ýan wasan kungiyar kwallon kafa ta kasa Super Eagle sukayi bazai kawo naqasu a...

Next Post
Martani Ga Arewa: Yarbawa Za Su Fara Yajin Aikin Cin Nama

Martani Ga Arewa: Yarbawa Za Su Fara Yajin Aikin Cin Nama

Da Ɗumi-Ɗumi: Abinda Ɗaliban Makarantar Jangeɓe Suka Ce Bayan Samun Yanci

Wadanda Suka Sace Mu Sun Nemi Auren mu, Sun Ba Mu Lambobin Wayarsu - ‘yan matan makarantar Jangebe

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In