">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Saturday, August 16, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Akwai Yiwuwar Gwamnoni Su Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga

by Abubakar Ismail kankara
February 25, 2021
in Best Store, Devices, Geek Ideas, Sport Stories
0
Akwai Yiwuwar Gwamnoni Su Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga
Share on FacebookShare on Twitter
">

Manyan alamu sun bayyana cewa Kungiyar gwamnonin Najeriya na wani shiri domin yin zaman sulhu da miyagun ‘yan bindiga dake addabar kasar musamman yankin Arewacin Kasar da nufin kawo zaman lafiya dawamamme a faɗin Najeriya.

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Najeriya Dr. Kayode Fayemi ya nuna yiwuwar yin hakan a ranar Talata, bayan ya kai wa gwamnan Jihar Neja, Abubakar Sani Bello ziyarar jaje na garkuwa da ɗaliban Makarantar Kagara da ‘yan Bindiga suka yi.

Gwamna Kayode Fayemi ya ziyarci abokin aikin na sa ne tare da wasu takwarorinsa a garin Minna. Hakan na zuwa bayan garkuwa da mutanen da aka yi a jihar.

“Duk mun san irin ciwon da ka ke ji a zuciya. Mun kuma san tsoro da dar-dar din da mutanen jihar Neja su ka shiga.”

RelatedPosts

Gobarar Tankar Fetur Ta Yi Ajalin Mutane da Dama a Neja

Iyalan Waɗanda Harin Sojoji ya Shafa a Zamfara Sun Nemi Diyya da Tallafi

Kananan Hukumomi Za Su Fara Karɓar Kuɗaɗensu Kai Tsaye – Fadar Shugaban Ƙasa

Kano Ta Dauki Matakan Gaggawa Kan Rahoton Cutar Murar Tsuntsaye

“Wannan ba bakon abu ba ne. Abin da ya faru ya taba faru wa da wasu. Ka na cikin tawagar da ta kai ziyarar jaje Jihar Borno, Katsina Ogun da Oyo.”

Gwamna Fayemi ya ƙara da cewa bai so a rika yawan koka wa, wannan ba shi ne abin da ya kamata ba. “Mutanenmu na neman yadda za a bi a kawo karshen wannan tashin hankali ne kawai.”

“Dole kuma mu duba sauran bangarori daban da aikin da jami’an tsaro su ke yi, idan hakan ya na nufin ayi sulhu ne to ba makawa za mu yi shi.

Shugaban Gwamnonin ya tabbatar da cewa za su yi duk abin da ya kamata domin ganin wannan rikici ya zama tarihi. “Sai mun duba abubuwan da su ka fara sababba wannan rikicin domin gano bakin zaren.

Da yake maida jawabi, gwamnan jihar Neja Abubakar Sani Bello ya ce ya goyi bayan kiran Ƙungiyar Gwamnonin na cewa ayi sulhu, ya ce amma idan har za ayi hakan, a zauna a sasanta ne da tubabbun ‘yan bindigan.

Tawagar Ƙungiyar Gwamnonin da suka ziyarci Jihar sun haɗa Gwamnan Simon Lalong na Jihar Filato, Abdulrahman Abdulrazaq na Kwara sai Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa da gwamna Aminu Waziri Tambuwal na jihar Sokoto.

A baya dai kun ji yadda Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna ya bayyana cewa bai gamsu da matsayar Ahmad Gumi, na cewa gwamnatin tarayya ta zauna teburin sasanci da miyagu ba.

">
">

Gwamnan na Jihar Kaduna, ya ce ba’a sulhu da ‘yan ta’adda kuma bai yarda a yi musu afuwa ba. “Ban yarda da wannan ba, miyagun ‘yan bindiga ne, mafi yawancinsu a jeji su ke, mu gano su, mu je mu yi maganinsu.”

DAILY EPISODE

BIYOMU A FACEBOOK DA TWITTER

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail kankara

Abubakar Ismail Kankara is the founder and CEO of AIACCESS Contractors and the Managing Editor OF Daily Episode

Related Posts

Gobarar Tankar Fetur

Gobarar Tankar Fetur Ta Yi Ajalin Mutane da Dama a Neja

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Mutane da dama, ciki har da wata mai juna biyu, sun rasu yayin da gobara ta tashi lokacin da suke...

harin jiragen Sojin

Iyalan Waɗanda Harin Sojoji ya Shafa a Zamfara Sun Nemi Diyya da Tallafi

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Iyalan waɗanda harin jiragen Sojin saman Najeriya ya rutsa da su a Zamfara sun nemi gwamnati ta biya su diyya...

Asusun Bai Ɗaya

Kananan Hukumomi Za Su Fara Karɓar Kuɗaɗensu Kai Tsaye – Fadar Shugaban Ƙasa

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Fadar shugaban ƙasa ta sanar da cewa, daga ƙarshen watan Janairu, dukkan kananan hukumomi a Najeriya za su fara karɓar...

Murar Tsuntsaye

Kano Ta Dauki Matakan Gaggawa Kan Rahoton Cutar Murar Tsuntsaye

by Abubakar Ismail kankara
January 17, 2025
0

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta yi kira ga al’umma da su kwantar da hankali tare da kai rahoton duk...

Biden da Netanyahu sun tattauna kan tsagaita wuta a Gaza

Biden da Netanyahu sun tattauna kan tsagaita wuta a Gaza

by Abubakar Ismail kankara
January 13, 2025
0

Shugaban Amurka, Joe Biden da Firaiministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu sun tattauna ta waya a daidai lokacin da ake ci gaba...

rikicin masarautar Kano

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Umarci Sake Sauraron Shari’ar Rikicin Masarautar Kano

by Abubakar Ismail kankara
January 10, 2025
0

Kotun ɗaukaka ƙara da ke Abuja ta bayar da umarnin sake sauraron shari’ar rikicin masarautar Kano da ya haɗa da...

Next Post
Ko mutuwa nayi Zan roki Allah ya dawo Dani amatsayin dan fulani, mu fulani ba ‘yan ta’adda bane ~ Sarkin musilmi 

Ko mutuwa nayi Zan roki Allah ya dawo Dani amatsayin dan fulani, mu fulani ba ‘yan ta’adda bane ~ Sarkin musilmi 

Zamu tabbatar mun kwato kudaden Nageriya daga hannun barayin Gwamnati – Abdulrasheed Bawa

Zamu tabbatar mun kwato kudaden Nageriya daga hannun barayin Gwamnati - Abdulrasheed Bawa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In