">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Wednesday, October 15, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Sabbin Tuhumar Da Kotu Ta Yi Wa Sheikh Abduljabbar, Yadda Zaman Ya Kaya

by Maryam Umar Said
September 2, 2021
in Uncategorized
0
Sabbin Tuhumar Da Kotu Ta Yi Wa Sheikh Abduljabbar, Yadda Zaman Ya Kaya
Share on FacebookShare on Twitter
">

RelatedPosts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

">
">

A yayin zaman da babbar kotun Addinin musulunci da ke kofar kudu tayi, qarqashin jagorancin Mai Shari’a Sarki Ibrahim Yola, a ranar Alhamis da misalin qarfe 9:20 na safe, inda aka gabatar da sabbin tuhumomi guda hudu ga sheikh Abduljabbar.

Zaman ya kaya kamar haka:

Tuhuma ta farko ita ce: “Ranar 10 ga watan 8 a shekara ta 2018 Abduljabbar a unguwar Sani Mainagge a karatunka na Jauful Fara inda ka yi wa Annabi SAW kage na cewar a Hadisi na 1365 da na 1358 na sahihi Muslim cewa Annabi SAW fyade ya yi wa Nana Aisha, wanda hakan ya saba wa 382 (b) kundin tsarin shari’ar Musulunci ta 2000.”

Shiru ne ya biyo bayan tambayar inda Abduljabbar bai amsa ba, hakan ya sa kotu ta tambaye shi yaren da yake ji, amma nan ma bai ce komai ba.

Kotu ta ci gaba da yi masa tambaya har sau uku amma bata samu kowanne amsa daga Abduljabbar ba.

Tuhuma ta biyu: “Ranar 10 ga watan 8 2018, a karatunka na Jauful fara ka yi amfani da kalaman ɓatanci inda ka yiwa Annabi (SAW) kage kan aurensa da Ummu Safiya, ka ce Sahihi Muslim ya ce Annabi ya kwace wa wani mutum matarsa 1365, wanda hakan cin zarafi ne, laifi ne da ya saba wa sashe na 382(b)”

A wannan karon ma Abduljabbar shiru ya yi.

Alkali ya sake tambaya: “Shin ka yarda ka aikata laifi ko ba ka yarda ba?”

Abduljabbar ya yi shiru bai ce komai ba.

Tuhuma ta uku: “A ranar 10 ga watan 8 ta shekarar 2019, a darasinka na 93 ka yi amfani da kalaman ɓatanci cewar dole manzon Allah ya yi wa matarsa Safiyya ya aureta, wanda babu wannan hadisi kai ka kirkire shi. Kuma hakan ya saɓa wa sashe na 382 (b) na kudin tsarin Shari’ar Musulunci na Kano na 2000.”

Kan wannan tuhumar ma dai Abduljabbar bai ce komai ba.

Tuhuma ta hudu: “A darasinka na 90 da na 98 na karatun Jauful fara ka kaga wa Annabi laifin zina, inda ka ce wata mata ta nemi Annabi ya biya mata bukatarta, kuma ka ce ya yi hakan, wannan ya saɓa wa sashe na 382 na kundin hukunta laifuffuka na shari’ar Musulunci na 2000 ta jihar Kano.

Alkali Sarki Yola ya sake tambayar Abduljabbar ko ya yarda da aikata laifin amma ya yi shiru bai ce uffan ba.

Sabbin zarge-zarge guda hudun da aka karanta wa Sheikh Abduljabbar dai sun shafi zargin yin batanci da kuma cin zarafin Annabi Muhammad (SAW) ne yayin karatuttukansa na Jauful-Fara, inda kuma yaqi cewa komai.

Sai dai a cewar masu kara ya saba da tanade-tanaden sashe na 382(b) na Kundin Dokokin Shari’ar Musulunci na Jihar Kano na 2000.

Lauyan da ke kare Abduljabbar, Barista Saleh M. Bakaro ya shaida wa kotun cewa masu shigar da kara ba su da damar janye zarge-zargensu na farko domin su canza su da wasu sabbi ana tsaka da shari’ar.

Sai dai amsar alkalin ta kore qorafinsu in da ya ce suna da ikon yin hakan dogaro da sashe 390 (i) na kundin dokokin ACGL na 2015.

Alkali ya bada umarnin bincikar lafiyar kwakwalwa da kunnen Sheikh Abduljabbar saboda rashin amsawa kotu tambayoyin da ta yi masa.

Masu Kare wanda ake tuhuma sun bukaci daukaka kara, inda Alkali ya umarci a bai wa lauyoyin wanda ake kara kwafin shari’ar domin daukaka karar da suke bukata.

Ya kuma shaida cewar za a cigaba da sauraron karar du da haka.

Daga nan ya ɗage zaman shari’ar zuwa mako biyu masu zuwa, inda za a dawo kotu ranar 16 ga watan Satumbar 2021 domin ci gaba da shari’ar.

DAILY EPISODE HAUSA

KU BIYO MU A FACEBOOK DA TWITTER

Maryam Umar Said

Maryam Umar Said

Related Posts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

by Yahuza Bawage
October 6, 2025
0

A wasu yankuna da ke kudancin jihar Kaduna a arewacin Najeriya, mallakar fili, musamman na noma, wani abu ne da...

zaben cike gurbi

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Tun bayan kammala zaben cike gurbi da aka gudanar a fadin kasar nan, rundunar yan sandan jahar ta bayyana irin...

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Duba da yadda rashin magudadan ruwa ke sanadiyar rubtawar kabaruruka musamman a lokutan damina, al’ummar unguwar Dala da kewaye dake...

yunƙurin kashe kansa

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2025
0

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wani mutum mai shekara 50 da aka bayyana sunansa da Modu Isa ya...

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

by Abubakar Ismail kankara
August 16, 2025
0

A dai-dai lokacin da ake fama da yawan yaran da basa zuwa makaranta musamman a fadin arewacin kasar nan, mai...

Tsaro Ya Inganta

Kasa da Awa Ɗaya Bayan Ya Wallafa Cewa Tsaro Ya Inganta, ’Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shi

by Abubakar Ismail kankara
August 15, 2025
0

Rahotan da Daily Episode Hausa ta tattara daka jaridar idon mikiya na nuna da cewa, yan bindiga dake yawan kashe...

Next Post
Gwamna Masari Ya Canza Ma Motocin Haya kalar Fenti a Katsina

Gwamna Masari Ya Canza Ma Motocin Haya kalar Fenti a Katsina

Mataimakin shugaban jam’iyyar Apc na shiyyar Funtua ya yi taro da shugabannin mazabun shiyya (117) na Apc.

Mataimakin shugaban jam’iyyar Apc na shiyyar Funtua ya yi taro da shugabannin mazabun shiyya (117) na Apc.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In