">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Monday, October 13, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Riqaqqen ‘Dan Bindiga Ya Nemi Gwamnati Ta Biyashi Diyyar Asarar Da Aka Yi Masa – Katsina

by Maryam Umar Said
August 29, 2021
in Technologies
0
Riqaqqen ‘Dan Bindiga Ya Nemi Gwamnati Ta Biyashi Diyyar Asarar Da Aka Yi Masa – Katsina
Share on FacebookShare on Twitter
">

Arewacin Najeriya na cikin inna-naha, duba da yadda ayyukan ýan bindiga kullum abin yake qara ta’azzara.

A Jihar Katsina wani fitaccen ‘dan ta’adda mai garkuwa da mutane mai suna Usman Idris da aka fi sani da Ruga Kachallah, ya nemi a biya shi diyyar buhunhunan hatsin sa da jami’an ‘yan sanda su ka banka wa wuta, kafin a yi sulhu da shi.

Kachallah shi ne babban gogaggen dan ta’addan da ya hana Ƙaramar Hukumar Safana zaman lafiya da kewayen ta a Jihar Katsina.

A ranar 25 Ga watan Mayu ne, jami’an tsaro suka kai wa Kachalla sumame har gidan shi, sai dai anyi rashin sa’a ba su same shi ba, inda suka cinnawa gidan wuta, su ka ƙone buhunhunan hatsi. Sannan kuma suka tafi da matan sa guda biyu.

RelatedPosts

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 6 a Sakkwato

An kama matar da ake zargi da kai wa Bello Turji makamai daji a Zamfara

An Kashe Shahararren Dan Ta’adda Gwaska, Yayin Da Mazauna Yakin Yantumaki Ke Hijira Kan Tarar N30m Da Barazanar Kisa

Shugaba Buhari Ya Bukaci Shugabannin Tsaro Su Kawo Sabbin Dabaru Kan Tsaron Kasar Nan

Inda ‘yan garin saboda tsoro da fargabar abinda zai iya aikata musu yasa sukayi taron-dangi suka kashe wutar.

Wannan lamari ne fa ya fusata Kachalla, ya riƙa kama mutane, har sai da aka sakar masa matansa biyu sannan ya sake su. Kuma ya ƙara ƙaimi sosai wajen kama mutane ya na yin garkuwa da su, ana biyan sa diyya.

Sakamakon hakan ya sa Kachalla neman zaman sulhu tare da bada sharadin cewar a biya shi diyyar barnar da aka yi masa ta qona mai gida.

Sai dai kuma Rundunar ‘Yan Sandan Katsina ta yi fatali da buqatarsa, inda ta bayyana cewa sau huɗu ana zaman sulhu da Ruga Kachallah amma yana karya wa.

Rahotanni sun bayyana cewa, Kachalla yana da tarin ‘yan bindigar da su ke ƙarƙashinsa, waɗanda sun fitini garuruwa da ƙauyukan yankin da garkuwa da satar shanu da dukiyoyin jama’a.

Kachallah ya tara maqudan kudade da yake sana’o’i da dama a yankin Safana.

Ya mallaki motocin haya sosai waɗanda ake yi masa jigila garuruwan yankin ana tara masa kuɗaɗe.

Wannan sana’a da Kachalla ke yi ta samar wa matasa da dama aikin yi a kewayen. Kuma su na hamdala sosai ga Kachallah, wanda hakan ya qara mai farin jini a wajen jama’ar yankin.

Mutanen karkarar Rulumbusawa, Yartsaku, Maƙera, Gimi da Chirena da ke cikin Ƙaramar Hukumar Safana a Jihar Katsina, sai sun nemi iznin Kachallah kafin su fita zuwa gonakin su.

A Arewacin Runka, gari na biyu wajen girma a Ƙaramar Hukumar Safana, can ma manoma sun miƙa wuya ga ‘Daular Kachallah’, gogarman ‘yan bindiga.

Ba kamar sauran ‘yan bindigar da ke ɓoye a cikin daji ba, shi Ruga Kachallah a cikin garin Gimi ya ke zaune da iyalin sa. Ya san kowa, kowa ya san shi.

Kwanan nan mazauna garin sun hana jami’an ‘yan sanda kama wani yaron sa, wani ɗan ta-kife, mai suna Gulbi.

An ce Kachallah na bai wa Gulbi shanun da ya sato, shi kuma ya na sayar masa.

Lokacin da mazauna garin su ka hana ‘yan sanda kama Gulbi, sun shaida wa Kwamandan Eriyar Safana, Dutsin-Ma, Ɗanmusa, Kurfi da Batsari, Aminu Umar-Daye cewa, ba za su bari a kama Gulbi ba, saboda idan aka kama shi, Kachalla cewa zai yi da haɗin bakin jama’a aka kama Gulbi, kuma a kan su zai huce haushin sa.

Haka dai Umar Daye ya haƙura ya janye ‘yan sandan.

Cikin 2016 ne Riga Kachalla ya haɗa kai da wasu fitinannun ‘yan bindiga da su ka haɗa har da Abdullahi Karki, wani tubabben ɗan bindiga a yanzu, su ka yi alƙawarin ajiye makamai a wani ƙwarya-ƙwaryan bikin karɓar tubar su a ƙarƙashin Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Mustapha Inuwa. An yi bikin a ƙauyen Illela, cikin Ƙaramar Hukumar Safana.

">

Sai dai kuma ba a daɗe da yin sulhun ba, sai dakarun Kachalla su ka koma bakin aikin kama mutane, su na yin garkuwa da su, ana biyan Kachalla kuɗaɗen fansa.

Bayan jami’an tsaro sun matsa lamba, wani dakaren Kachalla mai suna Jummah Tambai, ya kwashe iyalin sa ya koma Jihar Nassarawa, daga can kuma aka ce ya koma wani wurin da ake haƙar ma’adinai a cikin dajin Jihar Osun.

">

Haka shi ma mahaifin Kachalla da ke zaune a ƙauyen Sulluɓawa cikin Ƙaramar Hukumar Safana, ya yi hijira ya koma garin Banki cikin Ƙaramar Hukumar Anchau, saboda ya kasa hana ɗan sa Kachalla ci gaba da fashi, hare-hare da garkuwa da mutane.

DAILY EPISODE HAUSA

KU BIYO MU A FACEBOOK DA TWITTER

Maryam Umar Said

Maryam Umar Said

Related Posts

hallaka ’yan ta’adda

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 6 a Sakkwato

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Sojojin rundunar Operation Hadarin Daji sun hallaka ’yan ta’adda shida a wani artabu da ya faru a karamar hukumar Gudu,...

An kama matar da ake zargi da kai wa Bello Turji makamai daji a Zamfara

An kama matar da ake zargi da kai wa Bello Turji makamai daji a Zamfara

by Abubakar Ismail kankara
December 30, 2024
0

Bataliyar rundunar sojin Najeriya mai yaƙi da yan fashin daji a arewa maso yammacin Najeriya da ake kira da Operation...

yan bindiga

An Kashe Shahararren Dan Ta’adda Gwaska, Yayin Da Mazauna Yakin Yantumaki Ke Hijira Kan Tarar N30m Da Barazanar Kisa

by Abubakar Ismail kankara
February 11, 2022
0

Sama da mutane dubu daya mazauna kauyen Tashar Biri suka tsere daga kauyen da ke Yatumaki a karamar hukumar Dan...

Buhari Ya Nemi Shugabannin Tsaro Su Kawo Sabbin Dabaru Kan Tsaro

Shugaba Buhari Ya Bukaci Shugabannin Tsaro Su Kawo Sabbin Dabaru Kan Tsaron Kasar Nan

by Maryam Umar Said
September 8, 2021
0

A zaman da ya wakana a jiya Talata a fadar shugaban kasa kan yanayin tsaron kasar nan, shugaba Buhari ya...

Ýan Bindiga Sun Kai Sabon Harin Da Suka Yi Garkuwa Da Mutane 18 A Kaduna

Ýan Bindiga Sun Kai Sabon Harin Da Suka Yi Garkuwa Da Mutane 18 A Kaduna

by Maryam Umar Said
September 7, 2021
0

Ýan bindiga sun kai sabon hari a unguwar Keke da ke Karamar Hukumar Chikun ta Jihar Kaduna. Ýan bindigar sun...

Munyi Rashin Ýan Wasa Amma Hakan Bazai Kawo Mana Naqasu Ba – Ahmad Musa

Munyi Rashin Ýan Wasa Amma Hakan Bazai Kawo Mana Naqasu Ba – Ahmad Musa

by Maryam Umar Said
September 7, 2021
0

Canja shekar da wasu daga cikin ýan wasan kungiyar kwallon kafa ta kasa Super Eagle sukayi bazai kawo naqasu a...

Next Post
Yanzu Haka Kungiyar Taliban Tana Da Damar Mallakar Sama Da Dala Biliyan 85

Yanzu Haka Kungiyar Taliban Tana Da Damar Mallakar Sama Da Dala Biliyan 85

Aikin Ýan Bindiga Bai Shafi Yare Ko Addini Ba – El-Rufa’i

Aikin Ýan Bindiga Bai Shafi Yare Ko Addini Ba - El-Rufa'i

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In