">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Tuesday, October 14, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wadanda Suka Kashe Tsohon Kwamishina a Katsina

by Humaira Muhammad
July 30, 2025
in Labarai
0
Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wadanda Suka Kashe Tsohon Kwamishina a Katsina
Share on FacebookShare on Twitter
">
">

Babbar Kotun Jihar Katsina mai lamba 9, karkashin jagorancin Mai Shari’a I.I. Mashi, ta yanke hukuncin kisa ga mutum biyu da aka samu da laifi a kisan gilla da aka yi wa tsohon Kwamishinan Kimiyya da Fasaha na Katsina, marigayi Honourable Rabe Nasir, a shekarar 2021.

Kotun ta tabbatar da cewa Shamsu Lawal tsohon mai gadin marigayin da Tasi’u Rabi’u wanda ke aikin girki a gidan mamacin sun bai wa Rabe Nasir abinci mai guba wanda ya kashe masa jiki don ya gaza komai sai yanda akai da shi, wanda ya janyo mutuwarsa, bayan an samu damar caccaka masa wuƙa. Hakan ya tabbata ne bisa binciken da asibiti ta gudanar, wanda ya nuna akwai guba a jikin mamacin, da kuma hujjojin binciken ‘yan sanda.

Baya ga hukuncin kisa da aka yanke wa mutum biyun, kotun ta kuma yanke hukuncin dauri na shekaru biyar a gidan yari ga wani tsohon mai gadi, Sani Sa’adu, bayan da aka same shi da laifin boye gaskiya game da lamarin kisan.

A gefe guda, kotun ta sallami wata yarinya mai suna Gift Bako, wadda aka kasa gabatar da hujjoji masu gamsarwa da ke da nasaba da laifin. Lauyanta, Barista Shedrack, ya yaba da hukuncin kotun, yana mai cewa hukuncin ya tsaya kan gaskiya. Haka kuma, lauyoyin dukkan ɓangarorin sun bayyana gamsuwarsu da yadda shari’ar ta gudana da kuma hukuncin da aka yanke.

RelatedPosts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

Lauyan waɗanda aka samu da laifi, Barista Ahmad Murtala Kankia, ya roƙi kotu da ta yi sassauci a hukuncin, yana mai jaddada cewa wadanda lamarin ya shafa na da nauyin iyaye da iyali da ke dogara da su. Sai dai, lauyar masu gabatar da kara, ta nuna jin daɗinta da hukuncin, inda ta ce ya yi daidai da doka kuma an samu adalci.

Wakilan Katsina Times da suka halarci zaman kotun sun shaida cewa wadanda aka yankewa hukuncin sun shiga cikin firgici lokacin da jami’an tsaro suka shigar da su cikin mota domin wucewa da su gidan yari. Haka zalika, an hangi farin ciki da jin daɗi a fuskar ‘yan uwa da lauyoyin Gift Bako bayan kotun ta wanke ta daga zargin.

Marigayi Rabe Nasir ya rike mukamin Kwamishinan Kimiyya da Fasaha a Jihar Katsina a lokacin gwamnatin tsohon Gwamna Aminu Bello Masari. Haka kuma, ya kasance ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Mani da Bindawa a shekarar 2003, tare da riƙe mukamin jami’in hukumar DSS a baya.

">

A bangare guda, akwai wasu mutane biyu da ke da hannu a shari’ar, da suka kai kara a Babbar Kotun Kaduna, suna neman dakatar da cigaban shari’ar a Katsina.

DAILY EPISODE HAUSA

Humaira Muhammad

Humaira Muhammad

Related Posts

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

Daga Aikatau Zuwa Mallakar Filaye: ‘Matan da ke Alfahari da Sauyin da Suka Samu’

by Yahuza Bawage
October 6, 2025
0

A wasu yankuna da ke kudancin jihar Kaduna a arewacin Najeriya, mallakar fili, musamman na noma, wani abu ne da...

zaben cike gurbi

Yan sanda a Kano Sun Gurfanar da Mutane 333 Da Aka Kama Lokacin Zaben Cike Gurbi a Kotu

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Tun bayan kammala zaben cike gurbi da aka gudanar a fadin kasar nan, rundunar yan sandan jahar ta bayyana irin...

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

Yadda Aka Gudanar da Aikin Gyaran Makabarta a Dala

by Abubakar Ismail kankara
August 18, 2025
0

Duba da yadda rashin magudadan ruwa ke sanadiyar rubtawar kabaruruka musamman a lokutan damina, al’ummar unguwar Dala da kewaye dake...

yunƙurin kashe kansa

Wani Magidanci Yayi Yunƙurin Kashe Kansa Tare da Yanke Al’aurarsa Sabida Matar Daya Saka Taki Amincewa Ta Dawo

by Abubakar Ismail kankara
August 17, 2025
0

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wani mutum mai shekara 50 da aka bayyana sunansa da Modu Isa ya...

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

by Abubakar Ismail kankara
August 16, 2025
0

A dai-dai lokacin da ake fama da yawan yaran da basa zuwa makaranta musamman a fadin arewacin kasar nan, mai...

Tsaro Ya Inganta

Kasa da Awa Ɗaya Bayan Ya Wallafa Cewa Tsaro Ya Inganta, ’Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shi

by Abubakar Ismail kankara
August 15, 2025
0

Rahotan da Daily Episode Hausa ta tattara daka jaridar idon mikiya na nuna da cewa, yan bindiga dake yawan kashe...

Next Post
Tsaro Ya Inganta

Kasa da Awa Ɗaya Bayan Ya Wallafa Cewa Tsaro Ya Inganta, ’Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shi

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Sarkin Rano Ya Haramtawa Iyaye Aurar da ’Ya’ya Mata Kafin Kammala Makarantar Firamare

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In