‘Yan Fansho sun rubutawa Shugaba Muhammadu Buhari wasika, karkashin lemar kungiyarsu.
Wasikar dai ta godiya ce da yabawa ga shugaban kan biyan wasu daga cikin basussukan da suke bin gwamnati.
Wasikar wadda shugaban kungiyar Elder Actor Zal, da sakatare suka rattaba wa hannu, sun bayyana Shugaba Buhari a matsayin shugaban da ke jin koken talakawansa, kuma hakan ya nuna kokarin da gwamnati ke yi na ganin ‘yan fanshon su ma sun dara.
Wasikar ta ce: ”A madadin shugabannin wannan kungiya da mabobinta baki daya muna mika sakon godiya ga Shugaba Muhammadu Buhari, kan ba da umarnin biyanmu hakkokin mu na shekaru biyu, duk da halin matsin da tattalin arzikin Najeriya ke ciki.
“An ba da umarnin biyanmu na watanni 12, sai kuma wasu watanni 6 a watan Yuni, da kuma karin wasu watanni 6 da muke sa ran karba a kowanne lokaci.”
Wasikar ta kara da cewa su na fatan nan ba da jimawa ba za su karbi ragowar kudin watanni 6 ba tare da bata lokaci ko samun wata matsala.
“A karshe wasi kar ta karkare da cewa, “Ba mu da kalmar da za mu gode maka da ita.”
KU BIYO MU A FACEBOOK DA TWITTER