">
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
Monday, October 13, 2025
No Result
View All Result
NEWSLETTER
Daily Episode Hausa
-18 °c
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu
No Result
View All Result
Daily Episode Hausa
No Result
View All Result
">

Kano: Ana jan ƙafa wajen gano ƴaƴanmu da aka sace – Iyaye

by Maryam Umar Said
August 3, 2021
in Sport Stories
0
Kano: Ana jan ƙafa wajen gano ƴaƴanmu da aka sace – Iyaye
Share on FacebookShare on Twitter
">

Ƙungiyar iyayen yaran da aka sace a Kano ta zargi kwamitin da gwamnati ta ɗora wa alhakin gano sauran yaran da aka sace a jihar daga shekarar 2010 zuwa 2019 da jan ƙafa wajen fitar da sakamakon gwajin ƙwayar hallitta da aka yi wa yaran don tantancewa.

Koken ƙungiyar na zuwa ne bayan da a makon da ya gabata wata kotu da ke jihar Kanon ta yankewa Mista Paul da ake zargi da sace yaran jihar yana safarar su zuwa jihohin kudancin Najeriya, hukuncin ɗaurin sama da shekara 100 a gidan kaso.

Sakataren kungiyar iyayen da aka sace wa ƴaƴa, Shu’aibu Ibrahim Tajiri, ya shaidawa BBC cewa tsawon lokacin da aka ɗiba wajen samar da sakamakon gwajin kwayar hallittar yara 10 da aka gano a jihar Anambra, ya nuna cewar kwamitin ba da gaske yake aikinsa ba.

Tajiri ya ce kimanin wata shida kenan da daukar ƙwayoyin hallatar yaran da aka gano a jihar ta Anambra, amma sun gaji da yau da gobe da yan kwamitin ke yi musu, inda suka ce da rabon kwamitin ya zauna an fi wata uku.

RelatedPosts

Gobarar Tankar Fetur Ta Yi Ajalin Mutane da Dama a Neja

Iyalan Waɗanda Harin Sojoji ya Shafa a Zamfara Sun Nemi Diyya da Tallafi

Kananan Hukumomi Za Su Fara Karɓar Kuɗaɗensu Kai Tsaye – Fadar Shugaban Ƙasa

Kano Ta Dauki Matakan Gaggawa Kan Rahoton Cutar Murar Tsuntsaye

To sai dai a cewar kwamitin gano inda yaran da aka sacen suke, ya ce suna aiwatar da shawarwarin da suka bai wa gwamantin jihar kusan guda 40, ya ce suna aiki tuƙuru kan batun dawo da yaran kuma suna da gwajin kusan yara 6 daga cikin wadanda aka dauki kwayoyin hallartar tasu.

Sai dai kwamitin ya ce suna ci gaba da neman wata mata mai suna Amina Kagara wadda ta tsere tun bayan da aka bayar da ita belinta.

A makon da ya gabata ne dai wata babban kotun a Kano ta yanke wa Paul Owne, jagoran wadan da ake zargi da sace yara a Kano tare da sayar da su jihohin kudu hukuncin daurin shekaru 104 a gidan gyaran hali, bisa zargin aikata lafuka 38.

Haka zalika a ranar 31 ga watan Disambar bara ne dai iyayen wasu yara fiye da 100 da suka nemi ‘ƴa ‘ƴansu sama ko ƙasa a jihar Kano s ka gudanar da wata zanga-zanga tare da nuna damuwarsu kan yadda gwamnatin jihar ke jan kafa wajen ceto musu ‘ya’yan nasu.

Daga bisani a farkon shekarar da muke ciki ta 2021 gwamanti Kano ta bakin kwamishinan yada labaran jihar Mallam Muhammad Garba tace ta gano karin wasu yara 10 a jihar Anambra, kuma ta aike da jakadu dan tantance yaran na Kano ne.

Daga bisani, aka ce sai an yi gwajin kwayar hallitta, saboda samun wasu dake ikirarin wasu daga cikin yaran na Anambra ‘ya’yansu ne da suka bata.

">

DAILY EPISODE HAUSA

">

KU BIYO MU A FACEBOOK DA TWITTER

Maryam Umar Said

Maryam Umar Said

Related Posts

Gobarar Tankar Fetur

Gobarar Tankar Fetur Ta Yi Ajalin Mutane da Dama a Neja

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Mutane da dama, ciki har da wata mai juna biyu, sun rasu yayin da gobara ta tashi lokacin da suke...

harin jiragen Sojin

Iyalan Waɗanda Harin Sojoji ya Shafa a Zamfara Sun Nemi Diyya da Tallafi

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Iyalan waɗanda harin jiragen Sojin saman Najeriya ya rutsa da su a Zamfara sun nemi gwamnati ta biya su diyya...

Asusun Bai Ɗaya

Kananan Hukumomi Za Su Fara Karɓar Kuɗaɗensu Kai Tsaye – Fadar Shugaban Ƙasa

by Abubakar Ismail kankara
January 18, 2025
0

Fadar shugaban ƙasa ta sanar da cewa, daga ƙarshen watan Janairu, dukkan kananan hukumomi a Najeriya za su fara karɓar...

Murar Tsuntsaye

Kano Ta Dauki Matakan Gaggawa Kan Rahoton Cutar Murar Tsuntsaye

by Abubakar Ismail kankara
January 17, 2025
0

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta yi kira ga al’umma da su kwantar da hankali tare da kai rahoton duk...

Biden da Netanyahu sun tattauna kan tsagaita wuta a Gaza

Biden da Netanyahu sun tattauna kan tsagaita wuta a Gaza

by Abubakar Ismail kankara
January 13, 2025
0

Shugaban Amurka, Joe Biden da Firaiministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu sun tattauna ta waya a daidai lokacin da ake ci gaba...

rikicin masarautar Kano

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Umarci Sake Sauraron Shari’ar Rikicin Masarautar Kano

by Abubakar Ismail kankara
January 10, 2025
0

Kotun ɗaukaka ƙara da ke Abuja ta bayar da umarnin sake sauraron shari’ar rikicin masarautar Kano da ya haɗa da...

Next Post
Najerya ta karbi tallafin rigakafin korona miliyan 4 daga Amurka

Najerya ta karbi tallafin rigakafin korona miliyan 4 daga Amurka

Ƴan fansho sun yi wa Shugaba Buhari wasiƙar Godiya

Ƴan fansho sun yi wa Shugaba Buhari wasiƙar Godiya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

">
  • Talla
  • Tuntube Mu
  • Gida
TUNTUBE MU: 08032398985 info@dailyepisode.ng

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Tsaro1
  • Bincike
  • Siyasa
  • Qalubalen Mu
  • Aiki/Sana’a
  • Ra’ayi
  • Tuntube Mu

Copyright © 2025 DAILY EPISODE HAUSA Designed by AIACCESS CONTRACTORS

Login to your account below

Forgotten Password?

Fill the forms bellow to register

All fields are required. Log In

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In